Hukumar NCDC ta sanar da karin mutum 169 da suka kamu da cutar Korona a Najeriya ranar Alhamis.
Alkaluman da hukumar NCDC ta fitar ranar Alhamis sun nuna cewa Legas ta samu karin mutum –17, FCT-42, Kaduna-74, Kano-8, Ogun-6, Oyo-6, Rivers-6, Ekiti-3, Bauchi-3, Katsina-2, Delta-1 da Ondo-1
Yanzu mutum 66974 suka kamu da cutar a Najeriya, mutum 62,585 sun warke, 1,169 sun rasu. Sannan kuma zuwa yanzu mutum 3,220 ke dauke da cutar a Najeriya.
Har yanzu dai jihar Legas ne ke da mafi yawan wadanda suka kamu da mutum 23,083, FCT –6,671, Oyo – 3,721, Edo –2,696, Delta –1,824, Rivers 2,969, Kano –1,789, Ogun –2,202, Kaduna –3,019, Katsina -1,012, Ondo –1,728, Borno –745, Gombe – 938, Bauchi – 765, Ebonyi –1,055, Filato -3,813, Enugu – 1,332, Abia – 926, Imo –662, Jigawa – 331, Kwara –1,096, Bayelsa – 445, Nasarawa – 488, Osun –945, Sokoto – 165, Niger – 296, Akwa Ibom – 339, Benue – 496, Adamawa – 261, Anambra – 282, Kebbi – 93, Zamfara – 79, Yobe – 94, Ekiti – 357, Taraba- 157, Kogi – 5, da Cross Rivers – 90.
A cigaba da kokarin yadda za a dakile yaduwar Korona a Najeriya da kuma sanar wa mutane bayanan gaskiya game da annobar gwamnati tare da hadin guiwar UNICEF sun samar da wata layin kira na waya da za a rika samun labarin gaskiya game da cutar.
Mutum zai aika da sakon ‘Coronavirus’ zuwa lambar 24453, daga nan za a aiko masa da sakonni game da cutar da matsayin da duniya ke ciki da kasa Najeriya.
Domin shiga wannan dandali a facebook ko Kuma WhatsApp za a iya aikawa da sakon ‘Coronavirus’ zuwa ga +234 908 740 1607. Ko Kuma ta adireshin U-Report kamar haka @ureportnigeria
Wakilin asusun UNICEF a Najeriya Peter Hawkins ya gargadi mutane da su cigaba da kiyaye sharuddan guje wa kamuwa da cutar korona cewa yin haka ne kadai mutum zai iya samun kariya daga cutar.
Discussion about this post