• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TSAUTSAYI: Yadda ‘yan bindiga suka ware da Lami Awarware da Haulatu bayan halartar taron rantsar da Uba Sani a Kaduna

    Sojojin Najariya sun kara ragargaza wa Boko Haram motocin yaki bakwai

    Sojoji sun dagargaza matatun mai 47 sun kama barayin mai 65 – Hedikwatar tsaro na kasa

    HAJJI 2023: Yadda jirgin maniyyatan Jigawa ya koma Kano ba shiri, bayan ya samu matsala cikin sararin samaniyar Kamaru

    HAJJI 2023: Yadda jirgin maniyyatan Jigawa ya koma Kano ba shiri, bayan ya samu matsala cikin sararin samaniyar Kamaru

    GANAWAR TINUBU DA NLC: Ƙungiyar Ƙwadago ta ce a tilas a soke ƙarin kuɗin mai, an shammaci ‘yan Najeriya

    GANAWAR TINUBU DA NLC: Ƙungiyar Ƙwadago ta ce a tilas a soke ƙarin kuɗin mai, an shammaci ‘yan Najeriya

    Buhari-signing-2020-budget

    Gwamnatin tsohon shugaban kasa Buhari ta sanar da sabbin nade-nade a daidai ana rantsar da Tinubu shugaban kasa

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    2015-2023: ‘Na yi sukuwa ta lafiya, na kai zamiya lafiya’ – Buhari

    BANKWANA DA BUHARI: ‘Tinubu yau mafarkin ka ya zama gaskiya, Allah ya sa ka kai Najeriya fiye da inda na kai ta’ – Nasihar Buhari ga Asiwaju

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TSAUTSAYI: Yadda ‘yan bindiga suka ware da Lami Awarware da Haulatu bayan halartar taron rantsar da Uba Sani a Kaduna

    Sojojin Najariya sun kara ragargaza wa Boko Haram motocin yaki bakwai

    Sojoji sun dagargaza matatun mai 47 sun kama barayin mai 65 – Hedikwatar tsaro na kasa

    HAJJI 2023: Yadda jirgin maniyyatan Jigawa ya koma Kano ba shiri, bayan ya samu matsala cikin sararin samaniyar Kamaru

    HAJJI 2023: Yadda jirgin maniyyatan Jigawa ya koma Kano ba shiri, bayan ya samu matsala cikin sararin samaniyar Kamaru

    GANAWAR TINUBU DA NLC: Ƙungiyar Ƙwadago ta ce a tilas a soke ƙarin kuɗin mai, an shammaci ‘yan Najeriya

    GANAWAR TINUBU DA NLC: Ƙungiyar Ƙwadago ta ce a tilas a soke ƙarin kuɗin mai, an shammaci ‘yan Najeriya

    Buhari-signing-2020-budget

    Gwamnatin tsohon shugaban kasa Buhari ta sanar da sabbin nade-nade a daidai ana rantsar da Tinubu shugaban kasa

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    2015-2023: ‘Na yi sukuwa ta lafiya, na kai zamiya lafiya’ – Buhari

    BANKWANA DA BUHARI: ‘Tinubu yau mafarkin ka ya zama gaskiya, Allah ya sa ka kai Najeriya fiye da inda na kai ta’ – Nasihar Buhari ga Asiwaju

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

Yadda Gwamnonin Jahohi Ke Yi Wa Kananan Hukuma Mulkin Mallaka, Daga Kais Daud Sallau

Premium Times HausabyPremium Times Hausa
May 24, 2019
in Ra'ayi
0
Kais Daud Sallau

Kais Daud Sallau

Kananan hukumomi an kirkire su ne domin su samarwa al’umma da suke kauye da karkara saukin kai bukatun su zuwa ga gwamnatin jahar da na tarayya, domin samun cin gajiyar gwamnati cikin sauki ta hanyar shugaban karamar hukuma. Shugaban karamar hukuma tare da taimakawar wakilcin gunduma (councilor) sune tsani tsakanin gwamnatin jiha da al’ummar da su ke kauye ko karkara saboda nisan su da gwamnati.

Shuwagabannin kananan hukuma su suka fi sanin matsalolin al’umma, domin su ke tare da talakawa. Sune hukumomin gwamnati da talaka ke iya gani.

Kama daga gwamna zuwa shugaban kasa ba mutane ne wadanda ake ganin su cikin sauki ba. Kafin ka samu daman ganin gwamna ko shugaban kasa dole sai kai mai fada a ji ne, kokuma kana da alaka da wannan gwamnan ko shugaban kasa. Saboda da haka dole ta hanyar shugaban karamar hukuma gwamna zai san matsalar mutane da ke nesa da shi, shi kuma yaga shugaban kasa.

A baya zaka ga shugaban karamar hukuma na iya yi wa al’ummar shi aiki kama daga gina gota da gada, gina asibiti, gina makaranta, gina kasuwa, samar musu ingantaccen ruwa shan da sauran su. Amma yanzun zaka ga shugaban karamar hukuma zai hau mulki har ya sauka bazai yi wani aikin ko daya ba sakamakon mulkin mallaka da gwamnonin jahohi su ke yiwa kananan hukuma na sace kudaden kananan hukuma da gwamnatin tarayya su ke turo wa. Hakan ya taimaka gurin karancin ci gaba a matakin kananan hukuma, da kuma yawaitar rashin kudi.

Yadda Gwamnonin Jahohi Ke Yi Wa Kananan Hukuma Mulkin Mallaka

Gwamnonin jahohi sun mai da kananan hukuma gurin tatsan kudi, an kai matsayin da albashin ma’aikatan karamar hukuma gwamna ke biya ba shugaban karamar hukuma ba. Kawai shi shugaban karamar hukuma saide ya jira gwamna ya ba shi abinda da ya samu. Ba maganan tura mishi da kudin yi wa al’ummar shi aiki, kuma ba za su je su yi musu wani aiki ba.

Akasari idan kaji ance wannan gwamna yana aiki, toh duk bai wuce a cikin birnin jihar ya ke aiki ba, babu ruwan su da kananan hukumomin da suke karkashin. Su tsakanin su da kananan hukuma, su sace abinda gwamnatin tarayya ta ke turo musu duk wata.

Abinda ya sa gwamnoni baza su so a ce kananan hukuma sun samu ‘yancin kai ba shi ne, saboda kashi talatin da biyar (35%) cikin dari, koma sama da haka na kudaden da gwamnoni ke sacewa daga cikin kudaden kananan hukumomi ne da gwamnatin tarayya ke tura musu suke zantarewa ta hanyar asusun hadin kai tsakanin gwamnatin jihar da na kananan hukuma (Joint Account) saboda rashin imani da zalunci.

Ba wani abu a cikin asusun hadin kai na jiha da kananan hukuma (Joint Account) sai zalunci da sata. Da wannan asusu hadin kai ne gwamnonin jihohi su ke amfani su ke sace kudaden kananan hukuma. Misali idan ya kamata a turawa karamar hukuma naira miliyon hamsin (50m) ne, to, ta hanyar wannan asusun hadin kai na jiha da kananan hukuma (Joint Account) gwamna zai zaftare naira miliyon hamsin (50m) zuwa naira miliyon ashirin (20m), wannan ma a jihar da shuwagabannin kananan hukumomi su suke biyan albashin ma’aikatan karamin hukuma kenan ta hanyar biya a tebur (Table Payment). Amma a jihar da gwamnoni su ke biyan albashin ma’aikatan karamar hukuma ta hanyan banki (Bank Payment), toh bayan gwamna ya biya ma’aikatan karamar hukuma, sai de ya nima wani abin goro ya turawa shugaban karamin hukuma (Local Government Chairman). Kuma su shuwagabannin kananan hukumomin basu isa suyi magana ba saboda akasari hanyar da ake kawo su mulki akwai rashin adalci a ciki, ba zaban su a ka yi ba. Saboda haka dole su yi shiru.

Yana daya daga cikin mulkin mallakan da gwamnoni ke yi wa kananan hukuma kaga gwamna sai yayi shekaru uku da watanni kafin ya yi zaben kananan hukuma. Kawai gwamnati rikon kwarya su ke bayarwa domin su ji dadin kwashe kudin kananan hukumomin.

A cikin salon mulkin mallakan da gwamnoni ke yi wa kananan hukuma harda rashin biyan ma’aikatan kananan hukuma albashin. Akasari idan kaji ance gwamna bai biya ma’aikata albashi ba, toh zaka ga ma’aikatan karamar hukuma ne ba’a biya su ba, domin su ne wadanda gwamnoni su ka rena. Zaka ga gwamna yayi watanni shida koma fiye da haka baya biyan ma’aikatan kananan hukuma albashin su saboda zalunci da rashin imani. Bayan kowa yasan akasarin ma’aikatan karamar hukuma talakawa ne, kuma su ke tare da mafiyawan cin talakawa a karkashin su wadanda su suke daukar nauyin su kama daga ciyarwa, makaranta, kiwon lafiya da sauran su. Amma da yake su gwamnonin talaka ba shi ba ne a gaban su shiyasa su ke hana ma’aikatan albashin su, duk halin da zasu shiga su babu ruwan su.
Kais Daud Sallau.

Karin Karancin Albashi zuwa dubu talatin (30,000 Minimum Wage)

Yadda zaka kara ganewa cewa gwamnonin nan ba talakawa bane a gaban su, ka duka yadda su ke nuna bakin cikin su da adawa da karin albashi (Minimum Wage) wanda ake kokarin yi daga naira dubu goma sha takwas (18,000) zuwa dubu talatin (30,000). Wai saboda rashin imani wadansu gwamnonin wai basu da kudin da zasu biya wannan dubu talatin (30,000) na karamin albashi sai kace noma zasu yi su samo kudin. Wanda kowa yasan zuciyar su a mace ya ke, suma jira su ke daga gwamnatin tarayya a turo masu. Basu iya kirkiro yadda za su samo kudin shiga a jihar su ba, saide su jira a basu.

Kowa yasan yadda abubuwa suka kara kudi a kasan nan wanda duk mai imani ya san ma’aikata sun cancanci a kara musu albashi. Lokacin da ma’aikaci ya ke karbar dubu goma sha takwas (18,000) da yanzun kudin kaya ba daya ba ne. Amma wadansu gwamnoni saboda rashin tausayi suna bakin ciki da karin. Saboda sun san zai rage musu yawan kudaden da suke sacewa.

Su gwamnatin jihohin su zauna basu kirkiro hanyar shigowan kudi na matakin jihar (IGR) sun dogara ga kudin da gwamnatin tarayya su ke turawa saboda rashin kishi da son ci gaban jihar su. Shiyasa a ko da yaushe zaki ji su suna korafi cewa ba kudi, amma za ka gan su suna yin abubuwa na kudi idan wannan abin su zasu amfana da shi.

Toh Menene Mafita Game Da Lamarin Kananan Hukuma

Na farko,, kananan hukuma su samu yancin kansu wanda za’a dinga turo musu da kudaden na duk wata ba tare da ya bi ta hanun gwamna jiha ba. Ta nan ne suma shuwagabannin kananan hukuma zasu samu isassun kudaden da zasu yi wa al’umma aiki kamar yadda muka sani a baya.

Na biyu, samun yancin kai kananan hukuma na samun kudaden su daga gwamnatin tarayya kadai ba zai canza mulkin mallakan da gwamnoni ke yi wa kananan hukuma yadda ake so ba. Dole za’a yi doka wanda zai kasance zaben shuwagabannin kananan hukuma gwamnatin tarayya su zasu dinga gudanar da shi. Idan ba haka ba, toh kamar an kashe maciji ne ba’a yanke kan shi ba. Idan har ake ce za’a bar gwamnatin jihar su ci gaba da gudanar da zabukan kananan hukuma, toh ko tanan za’a ci gaba da tatse kudaden su. Domin gwamnoni zasu ci gaba da kawo yaran su, suna kwashe kudi suna kai mu, kokuma su ma ki yin zaben kamar yadda su ka saba. Saboda yan majalisun jahohi a aljuhun gwamnonin su ke, sai yadda su ka yi da su.

Na uku, dole kotur da za ta yi shari’ar zaben shuwagabannin kananan hukuma (Local Government Elections Tribunal) daga gwamnatin tarayya za’a kafa. Idan har za’a bar shi karkashin gwamnatin jiha, toh, tanan ma za’ayi abin da ake so.

Idan har za’a karbi wadannan abubuwa guda uku daga hanun gwamnatin jihar, toh da Ikon Allah talaka zai ga canji, kuma za’a samu ci gaba matuka a matakin kananan hukuma.

Daga karhe ina son ‘yan uwana talakawa su fahimci cewa, duk gwamna ko dan majalisar na tarayya ko jiha da baya goyon bayan samun yancin kai kananan hukuma, toh makiyin talaka ne.

Haka kuma duk gwamnan da baya goyon bayan karin albashi zuwa dubu talatin (30,0000 Minimum Wage) shima makiyin talakawa ne.

Saboda kashi tasa’in da biyar cikin dari (95%) na ma’aikatan karama hukuma talakawa ne. Babu yaron shugaban kasa, gwamna, Minista, ko komishina da yake aiki a karamar hukuma, kai ko shuwagabannin kananan hukuma ba kowa ya ke barin yaron shi yayi aiki a karamar hukumar ba.

Saboda haka duk wanda yayi adawa da samun yancin kananan hukuma da karin albashi zu dubu talatin, toh da talaka ya ke fada, mu shirya karan fadan mu, waton katin zabe (Voter’s Card) zuwa ranar zabe, sai mu nuna musu amfanin mu. Daman zaben 2023 iya ruwa fidda kai ne, kowa tashi ta fishe shi. Muna kallon iya takun kowa, katin zaben mu na ajiye. Ba suna ganin kamar suna da shekaru hudu ba, a gurin Allah kamar gobe ne.

A takaice wannan shi ne dan bayanin da zan yi akan yadda gwamnoni ke yi wa kananan hukuma mulki mallaka. Shiyasa ba za su goyi bayan shirin da a ke yi na zame su daga jikin su ba. Idan wani yaga abinda ya bata mishi rai yayi hakuri, idan anga kure, toh daman bamu fi karfin yin kuskure ba.

Allah ya ba mu zaman lafiya a kasar mu, ya ba mu damini mai albarka. Amen.

Tags: Gashin KaiHausaKAnsiloliKudiNajeriyaPREMIUM TIMES
Previous Post

Fayemi ya zama Shugaban Gwamnonin Najeriya, Dickon Shugaban Gwamnonin PDP

Next Post

RAHOTON MUSAMMAN: Yadda Manoman Najeriya ke noman tufa a cikin mawuyacin yanayi

Premium Times Hausa

Premium Times Hausa

Next Post
RAHOTON MUSAMMAN: Yadda Manoman Najeriya ke noman tufa a cikin mawuyacin yanayi

RAHOTON MUSAMMAN: Yadda Manoman Najeriya ke noman tufa a cikin mawuyacin yanayi

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • CIRE TALLAFIN MAI: Gwamnatin Kwara ta rage ranakun aiki ga ma’aikatan gwamnati
  • SITIYARIN TATTALIN ARZIKI: Tinubu, Tallafin Fetur da Amanar Jama’a Kan Siraɗi
  • RA’AYIN PREMIUM TIMES: Buƙatar korar Emefiele daga CBN da kuma yi wa bankin garambawul
  • ‘Ruhun Mai Tsarki ne ya umarce ni na kashe ta’ – Inji matar da ta kashe ‘yar shekara biyar
  • RIGA MALAM MASALLACI: Matasan Kano sun yi wa ginin ƴan canji diran mikiya, sun yi warwason kayan ‘ganima’

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.