Jam’iyyar APC mai mulki ta kara rasa ‘Yan Majalisar Tarayya har hudu, wanda suka fice daga cikin ta, suka koma wasu jam’iyyu.
Su hudun duk sun bayyana ficewar su daga APC a jiya Talata.
Adebayo ya koma AC, Williams ya koma LP, Adesina ya koma PDP yayin da Hassan ya koma ADC.
Jam’iyyar APC dai sai kara rairayewa ta ke yi, a kananan hukumomi, jiha da tarayya, tun bayan zaben fidda gwani da aka gudanar, wanda rikici da zarge-zargen magudi ya dabaibaye.
Discussion about this post