Rundunar ‘Yan sandan jihar Akwa-Ibom ta sanar cewa jami’an ta sun ceto wani jami’in hukumar zabe da wasu mutane 8 da aka yi garkuwa da su a jihar.
Kwamishinan ‘yan sandan jihar Adeyemi Ogunjemilusi, ya bayyana haka da yake zantawa da manema Labarai.
Adeyemi ya ce an sace wadannan mutane a kananan hukumomin Etim Ekpo da Ukanafun. Sannnan kuma jami’an sa sun farwa kwararon da ake zaton an boye su ne da karfe 12n dare inda Allah ya basu sa’ar ceto su duka.
Sunayen wadanda aka ceto
Eno Peter Udo, 50, of Ikot Inyang, Eno Itohowo Okon, 37, Ikot Inyang Abia, Imaobong Sunday Thomas, 14, Uduak Fred Obonukut, 45, Ikot Esop, Charity Moses Peter, 54, Ikot Ama Ikpe Annang, Etim Ekpo, Bessy Jimmy Okpon, 55, Esther Jimmy Okpon, 35, Ikot Inyang Abia, Ukanafun, abducted August 8, 20Otobong Sylvester Ukpong, 34, Iwukem, Etim Ekpo, Victoria Peter Udo, 50.
Discussion about this post