Minister Harkokin Kudi, Kemi Adeosun ta bayyana cewa Nijeriya ta kama hanyar fita daga halin matsin tattalin arziki da halin kaka-ni-ka-yi da ake ciki.
Kemi ta yi wannan jawabi ne a wurin wani gagarimin taron jin ra’ayoyi da amsa tambayoyin jama’a, wanda wasu ministoci suka shir ya, da yanzu haka ake cikin gudanarwa a Abuja.
Sauran Ministocin da ke wurin sun a amsa tambayoyin jama’a, sun hada da: Ministan Makamashi, Ayyuka da Gidaje, Fashola, Audu Ogbe Ministan Harkokin Noma, Lai Mohammed Ministan Yada Labarai, Udoma Udoma Ministan Kasafin Kudi da kuma Janar Dambazzau, Ministan Harkokin Cikin Gida.
Discussion about this post