Aƙalla ma’aikata 400 ne su ka rasa aikin su, bayan wata ambaliya ta lashe kaji fiye da 25,000 a wata katafariyar gonar kiwon kaji ta zamani.
An yi wannan gagarimar asara ce a wata gonar kiwon kaji da ke yankin Agbobo Ossomala, cikin Ƙaramar Hukumar Ogbaru, a Jihar Anambra.
Hakan ta haifar da rufe gonar kiwon kajin tare kuma da sallamar ma’aikatan gonar sama da mutum 400.
Baya ga kashe kaji fiye da 25,000, haka nan ta shafi ɓangaren kiwon kifi, noman dankali da sauran nau’ukan kayan abinci.
Shugaban gonar mai suna Patrick Sule-Ugboma shi ne ya bayyana wannan mummunan al’amari da ya shafi gonar ta sa mai suna Matuuci Farms Limited.
Ya bayyana haka a ranar Laraba, lokacin da ya ke zagayawa tare da manema labarai a cikin gonar, domin su gane wa idanun su irin gagarimar ɓarnar da ambaliyar ta yi.
Ya ce ya dakatar da ma’aikatan gonar su kimanin 400, sakamakon ambaliyar wadda ta faru a yankin na Ogbaru, inda yawanci mazaunan yankin su na rayuwa ne Kogin Neja, kuma su kan fuskanci ambaliya.
Sule-Ugboma ya ce gonar ta sa za ta kai faɗin hekta 20, kuma ya yi gagarimar asara mai ɗimbin yawa.
“Mun yi asarar sama da kaji 25,000, mun yi asarar kifaye na miliyoyin kuɗaɗe da sauran kayan gona na miliyoyin kuɗaɗe.”
Ya roƙi Gwamnatin Tarayya da Gwamnatin Jihar Anambra su gaggauta gyara gadar da ke yawan haddasa ambaliya a yankin, wadda ko a shekarar da ta gabata sai da ta ci rayukan jama’a.
Ya yi kira ga Gwamna Charles Soludo ya dubi irin matsananciyar rayuwar da yankin na su ke ciki.
Discussion about this post