Hedikwatar tsaron Najeriya DHQ ta bayyana cewa dakarun sojin Najeriya sun kashe ‘yan ta’adda 58 sannan sun kama wasu 161 a cikin makonnin biyu da suka gabata.
Darektan yada labarai na hedikwatar tsaro Musa Danmadami ya sanar da haka a Abuja ranar Alhamis.
Danmadami ya ce sojoji sun kama Kuma sun kashe wadannan mutane ne a yakin Arewa ta Tsakiya, Arewa maso Yamma da Arewa maso Gabashin Najeriya.
Ya ce dakarun sun ceto mutum 66 da ‘yan ta’addan suka yi garkuwa da su sannan sun kama makamai da dama da maharan ke amfani da su.
Danmadami ya ce dakarun dake aiki a karkashin ’Operation Hadin Kai’ sun kashe Boko Haram/ISWAP 26 da a ciki akwai dan kunan bakin wake daya, sun kama wasu mutum 22 da a cikin su akwai infoma biyu sannan sun kuma kama wasu ‘yan ta’adda 55 a yankin Arewa maso Gabas.
Ya ce dakarun sun ceto mutum 16 da aka yi garkuwa da su sannan iyalen maharan mutum 876 da suka hada da maza 89, mata 249 da yara 538 sun mika wuya.
Ya ce dakarun sun kama makamai da dama, motoci da dai sauran kaya a maboyar maharan.
“Rundunar sojin sama ta kashe ‘yan ta’adda da dama a harin da ta tai a sansanonin yan bindigan dake Arewa maso Gabas.
Danmadami ya ce rundunar ‘Operation Safe Haven’ da ‘Operation Whirl Stroke’ sun kashe ‘yan ta’adda 7, sun kama wasu 35 sannan sun ceto mutum 14 da aka yi garkuwa da su a Arewa ta Tsakiya.
Ya ce jami’an tsaron sun kama bindigogi da harsasai da dama da dabobbi 403 na sata.
Danmadami ya ce sojojin sama da kasa dake aiki a karkashin ‘Operation Hadarin Daji’ sun kai wa mahara hari a jihohin Kaduna, Katsina, Sokoto da Zamfara.
Ya ce a wannan harin dakarun sun kashe ‘yan ta’adda 25, sun kama 41 sannan sun ceto mutum 36 da aka yi garkuwa da su.
Discussion about this post