Kamfanin raba wutar lantarki dake jihar Enugu EEDC ya bayyana cewa a cikin makonni uku barayi sun lalata tiransifoma 20 a Kudu maso Gabashin kasar nan.
Kakakin kamfanin EEDC Emeka Ezeh ya bayyana haka a garin Enugu.
Ezeh ya ce kamfanin za ta hada hannu da jami’an tsaro domin ganin an hukunta barayin dake lalata tiransifoma.
Ya ce tun da kamfanin EEDC ta fara aiki babu ranar da Kamfanin ba sa ta samu labarin barayi sun lalata tiransifoma ba.
” Lalata tiransifoma da barayin ke yi ya kai har juye man tiransifoma suke yi baya ga sace wayoyi.
Ezeh ya ce duk barayin dake lalata tiransifoma da Kamfanin ta kama ta damka su ga hannun ‘yan sanda.
Ya yi kira ga mutane da su rika taimakawa kamfanin wajen sa Ido akan tiransifoma domin hana barayi lalata su.
Ezeh ya mika godiyarsa ga masu unguwani, kungiyoyin ‘yan sa kai da jami’an tsaro wajen ganin an kama wadanda ke lalata tiransifoma.
Discussion about this post