Hukumar NCDC ta bayyana cewa mutum sama da 18,000 sun kamu da cutar korona a dalilin rashin kiyaye sharuddan gujewa kamuwa da cutar da matafiya dake shigowa kasar nan ke yi.
Shugaban hukumar Ifedayo Adetifa ya sanar da haka ranar Juma’a a shafin hukumar dake yanar gizo.
Ya ce yin gwajin cutar na da mahimmanci domin kare lafiyar mutane da farfado da tattalin arzikin kasa.
Zuwa yansu mutum 251,684 ne suka kamu da cutar sannan mutum 3,123 sun mutu.
Bayan haka Adetifa ya yi kira ga mutane da su yi amfani da shafin da aka bude a duk lokacin da za su fita ko shigowa kasar nan.
Ya ce gwamnati na kokari wajen ganin ta gyara shafin domin ganin mutane sun yi rajista a duk lokacin da za su yi tafiya.
Adetifa ya yi kira ga duk mutane da su ci gaba da kiyaye sharuddan gujewa kamuwa da cutar domin dakile yaduwar cutar a kasar nan.
Discussion about this post