Babban Hadimin Shugaba Muhammadu Buhari kan Ayyukan Bunƙasa Yankin Neja Delta, Ita Enang ya bayyana cewa haƙiƙanin gaskiya a halin yanzu ba zai iya yin shisshigi ya ce ga a hannun hukumar da sakamakon binciken badaƙalar watandar kuɗaɗen Hukumar Bunƙasa Yankin Neja Delta ya ke ba.
Yayin da ya ke amsa tambayoyi masu zafi a Gidan Talabijin na Channels, a ranar Talata, Enag wanda tsohon Sanata ne daga Jihar Akwa Ibom ya ce, “abin da kawai zan iya cewa shi ne, kwamitin bincike ya gama aikin sa, kuma ya miƙa sakamakon bincike ga Shugaban Ƙasa, ta hannun Ministan Harkokin Shari’a, Abubakar Malami.”
Enag ya ce to daga nan ba zai iya cewa ga hannun ɓangaren hukumar da sakamakon binciken ya ke ba.
Idan ba a manta ba, cikin 2020 ne Premium Times Hausa ta riƙa bin-diddigin buga labarin badaƙalar watandar maƙudan biliyoyin nairori a Hukumar Bunƙasa Yankin Neja Delta, binciken da aka riƙa yi kai-tsaye a Majalisar Dattawa.
Makonni biyu da su ka gabata ne Buhari ya ce duk wanda ya ci kuɗi sai ya biya, kuma sai an ɗaure shi.
Shugaba Muhammadu Buhari ya bayyana da kakkausan harshe cewa dukkan waɗanda su ka ci kuɗaɗen Hukumar Bunƙasa Yankin Neja Delta (NDDC) sai sun amayar da su kuma za a hukunta su.
Buhari ya bayyana haka a Jihar Akwa Ibom, a lokacin da ya ke buɗe wani katafaren ginin ɗakin kwanan ɗalibai a Jami’ar Uyo.
“Bari na sanar da ku cewa duk waɗanda su ka ci kuɗin da aka ware domin inganta rayuwar al’ummar Neja Delta, sai sun amayar da kuɗaɗen. Kuma za a hukunta su.”
Haka Kakakin Yaɗa Labaran Shugaban Ƙasa Femi Adesina ne ya bayyana haka a ranar Alhamis.
Tuni dai Buhari ya bada umarnin a gudanar da binciken ƙwaƙwaf a NDDC, bayan samun rahoton cewa an yi shagalin da kuɗaɗen hukumar ta NDDD.
PREMIUM TIMES Hausa ta taɓa buga labarin yadda aka riƙa watandar maƙudan biliyoyin kuɗaɗe a NDDC.
An kuma gano yadda aka fara wasu ayyuka, amma aka watsar. Wasu kuma an nemi inda aka ce an fara su, amma ba a samu ko da wuri ɗaya ba a samu inda aka yi su.
Idan ba a manta ba, Ministan Bunƙasa Yankin Neja Delta, Godswill Akpabio ya taɓa cewa masu wawurar kuɗaɗe a NDDC sun maida kuɗaɗen hukumar kamar wata na’urar cirar kuɗi ta ATM machine, inda kowa ke cirar kudade irin yadda ya ga dama.
Adesina ya ce Hukumar Bunƙasa Yankin Neja Delta (NRC) ta gina gidan kwanan ɗaliban da Buhari ya bude a jami’ar.
Discussion about this post