• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    HANYAR DAMATURU ZUWA BIU: Yadda matafiya ke cin kwakwa Tsawon shekaru 9 an kasa kammala gyaran titin kilomita 125

    HANYAR DAMATURU ZUWA BIU: Yadda matafiya ke cin kwakwa Tsawon shekaru 9 an kasa kammala gyaran titin kilomita 125

    Kotu ta kwato maka-makan gidaje 48 a hannun tsohuwar Shugabar Hukumar NSITF

    KARKATAR DA NAIRA MILIYAN 289: EFCC ta gurfanar da wasu jami’an gwamnatin Katsina a kotu

    Gwamna Uba Sani ne ya yi  Ruwa ya yi Tsaki a takara ta ba mahaifina El-Rufai ba – Bello El-Rufai

    Gwamna Uba Sani ne ya yi Ruwa ya yi Tsaki a takara ta ba mahaifina El-Rufai ba – Bello El-Rufai

    FALLASA RUFA-RUFAR HADI SIRIKA: Majalisar Tarayya ta nemi Gwamnatin Tarayya ta dakatar da Nigeria Air

    FALLASA RUFA-RUFAR HADI SIRIKA: Majalisar Tarayya ta nemi Gwamnatin Tarayya ta dakatar da Nigeria Air

    Sanata Wamakko ya yi tir da kisan kiyashin da aka yi a tangaza, jihar Sokoto

    Sanata Wamakko ya yi tir da kisan kiyashin da aka yi a tangaza, jihar Sokoto

    Atiku ya kafa gaggan lauyoyi 18, ya ce su tashi tsaye su ƙwato masa ‘nasarar zaɓen sa’ daga hannun Tinubu

    SHARI’AR ZAƁEN SHUGABAN ƘASA: Atiku ya zargi INEC ta ƙin ba shi kwafen bayanan zaɓe duk da ya biya haƙƙin Naira miliyan 6 kuɗin karɓar bayanan

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TSAUTSAYI: Yadda ‘yan bindiga suka ware da Lami Awarware da Haulatu bayan halartar taron rantsar da Uba Sani a Kaduna

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    HANYAR DAMATURU ZUWA BIU: Yadda matafiya ke cin kwakwa Tsawon shekaru 9 an kasa kammala gyaran titin kilomita 125

    HANYAR DAMATURU ZUWA BIU: Yadda matafiya ke cin kwakwa Tsawon shekaru 9 an kasa kammala gyaran titin kilomita 125

    Kotu ta kwato maka-makan gidaje 48 a hannun tsohuwar Shugabar Hukumar NSITF

    KARKATAR DA NAIRA MILIYAN 289: EFCC ta gurfanar da wasu jami’an gwamnatin Katsina a kotu

    Gwamna Uba Sani ne ya yi  Ruwa ya yi Tsaki a takara ta ba mahaifina El-Rufai ba – Bello El-Rufai

    Gwamna Uba Sani ne ya yi Ruwa ya yi Tsaki a takara ta ba mahaifina El-Rufai ba – Bello El-Rufai

    FALLASA RUFA-RUFAR HADI SIRIKA: Majalisar Tarayya ta nemi Gwamnatin Tarayya ta dakatar da Nigeria Air

    FALLASA RUFA-RUFAR HADI SIRIKA: Majalisar Tarayya ta nemi Gwamnatin Tarayya ta dakatar da Nigeria Air

    Sanata Wamakko ya yi tir da kisan kiyashin da aka yi a tangaza, jihar Sokoto

    Sanata Wamakko ya yi tir da kisan kiyashin da aka yi a tangaza, jihar Sokoto

    Atiku ya kafa gaggan lauyoyi 18, ya ce su tashi tsaye su ƙwato masa ‘nasarar zaɓen sa’ daga hannun Tinubu

    SHARI’AR ZAƁEN SHUGABAN ƘASA: Atiku ya zargi INEC ta ƙin ba shi kwafen bayanan zaɓe duk da ya biya haƙƙin Naira miliyan 6 kuɗin karɓar bayanan

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TSAUTSAYI: Yadda ‘yan bindiga suka ware da Lami Awarware da Haulatu bayan halartar taron rantsar da Uba Sani a Kaduna

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

TONON SILILIN TASHOSHIN JIRAGEN RUWA: Yadda kwangilolin biliyoyin nairori su ka hada Amaechi da Hadiza Bala kakudubar rikici

Ashafa MurnaibyAshafa Murnai
May 11, 2021
in Babban Labari, Rahotanni
0
HADIZA BALA: Yadda Buhari da Amaechi suka karairaya dokar yadda ake tuhuma da dakatar da jami’in gwamnatin Tarayya

Ashe dai kwatagwangwamar rikicin kwangilolin biliyoyin nairori ne su ka hada dakatacciyar Shugabar Hukumar Tashoshin Ruwa Hadiza Bala rikici ita da ogan ta, Ministan Sufuri, Rotimi Amaechi.

Wasu gangariyar kwafen takardun da PREMIUM TIMES HAUSA ta damke a matsayin hujja, sun nuna cewa watanni kadan kafin dakatar da Hadiza a makon da ya gabata, ta tafka kadabolon rikici ita da Amaechi, kan wata gawurtacciyar kwangila.

Kakudubar rigima ta harde a tsakanin su, har sai da ta kai Ofishin Tantance Hakikanin Farashin Kwangila (BPP), Ministan Shari’a Abubakar Malami da Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Kasa, Ibrahim Gambari duk sun sa baki a rigimar.

Gambari ya aika wa Amaechi da Hadiza da umarni daga Shugaba Muhammadu Buhari, kuma ya nemi shawara daga waje, domin sasanta lamarin.

Hadiza wadda aka dakatar da ita tare da Minista Amaechi ya yi ikirarin cewa ta kasa cike gibin naira biliyan 165 da su ka kamata ta zuba asusun Gwamnatin Tarayya, ta maida raddin cewa lissafin da Amaechi ya dogara da shi, lissafi ne amma na dawakan-Rano.

Gurungunduma Da Kwatagwangwamar Kwangilar Da Ta Hada Amaechi da Hadiza Bala Zare Wa Juna Idanu:

Dalla-dallar abin da PREMIUM TIMES HAUSA ta gani da idon ta, wato akwai wata narkekiyar kwangila wadda NPA ta rubuta wa Hukumar Tantance Tantagaryar Adadin Kudaden Kwangila (Bureau of Public Procurement, wato BPP), inda ta nemi a zabi kamfani daga cikin wasu kamfanoni 9 da su ka nemi kwangilar aikin yashe gaba da gangar bakin mashigar jiragen ruwa a gefen teku a Lagos. Bonny, Warri da Gundumar Excravos.

PREMIUM TIMES HAUSA ta gano cewa kudaden wannan kwangila sun kai naira biliyan 65. Kwangilar yasar rairayi da dagwalon kwatamin gefen tekun Lagos ta kai naira biliyan 31. Ita kuma kwangilar yasar rairayi da dagwalon kwatami a Tashar Ruwa ta Bonny, ta kai naira biliyan 34.

NPA ta ce ta nemi bin tsarin zaben kamfanin da ya dace ya yi aikin, saboda yanayin irin aikin. Sannan kuma kwangilar aikin hada-ka da ake yi tsakanin Kamfanin Kula da Yasar Yashi na Lagos, LPCMC da na Bonny, wato BCN, duk wa’adin cikar aikin su ya kare cikin Disamba, 2019 da kuma Yuni 2020.

Hukumar Tantance Tantagaryar Adadin Farashin Kudaden Kwangila, BPP ta amince da tsarin da NPA ta ce a bi wajen bayar da kwangilar.

Katsalandan Daga Amaechi:

Amincewar ke da wuya sai Amaechi ya ce bai yarda da tsarin da aka bi ba, kuma nan take ya soke kwangilar, sannan ya ce kamfanin da ke kan kwangilar wadda wa’adin ta ya cika, to a kara masa wa’adin shekara daya.

Amaechi ya ce ya yi haka ne bisa shawarar da ya ce BPP ta Hukumomin Gwamnati sun bayar, bisa dalili na barkewar cutar korona.

Ita kuma Hadiza ta rubuta a cikin wani bayani cewa Minista Amaechi ya yi korafin cewa an maida shi saniyar-ware wajen tsara bayar da kwangilar, kuma ya nuna damuwa dangane da zunzurutun kudaden da aka ware don biyan kwangilolin.

Sannan kuma Hadiza ta ce kamfanonin da Amaechi ya ce a kara wa wa’adin shekara daya, sun shafe shekaru 15 su na wannan aiki. Ga shi kuma wa’adin su ya kare a Agusta.

Sannan kuma Hadiza ta ce babu wani dalili da Minista Amaechi zai kafa hujja da cutar korona domin dukkan aikin tantance kwangilolin ta sakon kar-ta-kwana na tsarin aiken ‘courrier’ aka yi shi.

Daga nan sai ta ce idan Amaechi bai gamsu da kwangilar ba, zai iya umartar NPA a ka’idance ta soke kwangilar sannan ta kara wa kamfanonin da wa’adin su ya kare shekara daya.

Cikin wata wasika a ranar 2 Ga Yuni, 2020, ana tsakiyar korona, Ma’aikatar Sufuri ta umarci NPA ta janye sanarwar neman kamfanonin da za a bai wa kwangilar aikin yashe rairayin.

Wani Daraktan Kula da Harkokin Shari’a da Barutuwan Koru na Ma’aikatar Sufuri, mai suna Pius Oteh ne ya sa wa takardar hannu.

Kuma ya umarci NPA ta kara wa kamfanonin da ke kan aikin yashe rairayi da dagwalon gefen teku wa’adin shekara daya.

Nan take NPA ta bi umarnin da Ma’aikatar Sufuri ta bayar.

“Mu Ke Da Ikon Soke Kwangila, Ba Ma’aikatar Sufuri Ba” -BPP

Ganin umarnin da Minista Amaechi ya bai wa NPA, sai Hukumar BPP ta rattaba cewa, “akwai fa ayyukan da cutar korona ba za ta hana aiwatar da su ba, kuma BPP din ce ke da iznin soke kwangiloli ba Ma’aikatar Sufuri a karkashin Amaechi ba.”

WASIKAR BPP Ga NPA: “Ba Ma’aikatar Sufuri ke da hakkin soke kwangila ba, hakkin Hukumar BPP ne. Maimakon a soke kwangila, a kara wa’adin watanni shida, yadda zai zamana an samu bin tsarin tallata masu sha’awar yin kwangila kamar yadda kasashen duniya su ka tsara cewa a rika bi.

“Amma idan Hukumar NPA na ganin cewa soke kwangilar shi ne mafi alheri ga kasar nan da daukacin jama’ar ta, to za ta iya dakatar da kwangilar.”

Hukumar NPA karkashin Hadiza Bala ta saki umarnin Minista Amaechi ta bi umarnin Hukumar BPP. Ta ci gaba da tallata neman ‘yan kwangilar da kamfanonin da za su shiga takarar neman aikin kwangilar, wato ‘bidding’ kenan a Turance.

Sai dai kuma ana cikin aikin tantance kamfanonin ne aka dakatar da Hadiza Bala daga shugabancin NPA, tare da kafa mata kwamitin bincike.

PREMIUM TIMES HAUSA ta gano cewa an samu sabani kuma tsakanin Amaechi da Hadiza Bala dangane da gaban-gabarar da Hadiza din ta yi ta soke ayyukan da Intels, kamfanin Atiku Abubakar ke yi a Tashoshin Jiragen Ruwa.

PREMIUM TIMES HAUSA ta gano cewa Minista Amaechi bai goyi bayan a kori Intels ba, amma Hadiza ba ta bi turba daya da ministan ba.

Tags: BPPGoyiHadizaIntelsNajeriyaPREMIUM TIMES
Previous Post

KORONA: Za a fara yi wa mutane allurar rigakafin cutar a zango na biyu a Najeriya – In ji Shu’aib

Next Post

ABUJA: A yi sallar Idi a masallatan Juma’ar unguwanni, babu zuwa filin Idi

Ashafa Murnai

Ashafa Murnai

Next Post
Eid Prayer

ABUJA: A yi sallar Idi a masallatan Juma'ar unguwanni, babu zuwa filin Idi

Discussion about this post

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • ƘARFIN HALI: Na san Kwankwaso na Villa yau, amma da mun haɗu da na gaura masa mari – Ganduje
  • ‘Yan sanda sun kama mutum 57 da suka kwashe ‘ganimar’ kayan gine-ginen da aka rusa a Kano
  • NUC ta baiwa Farfesa Gwarzo shaidar amincewa da fara karatu a jami’o’in Canadian, Abuja da Franco-British, Kaduna
  • SHARI’AR ZAƁEN SHUGABAN ƘASA: Peter Obi na so kotu ta ba shi iznin yi wa wasu jami’an ICT na INEC tambayoyi
  • TATTALIN ARZIKI: Ɗanyen man Najeriya ya fara kwantai a duniya, bayan Chana, Turai da Indiya sun koma sayen na Rasha mai rahusa sosai

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.