Tsohon gwamnan jihar Abia, Uzo Orji Kalu ya bayyana cewa yana kwaunar gwamnan jihar Enugu Ifeanyi Ugwuanyi saboda girmama Buhari da yake yi a ko da yaushe.
Kalu ya ce a duk lokacin da ya shigo jihar yakan leka gwamna Ifeanyi na Enugu.
” Ni fa Ifeanyi kamar dan uwa yake a wuri na saboda haka zumuntan mu ya wuce yadda mutane ke dauka.
” Duk lokacin da na garzayo garin Enugu, zan leko mu gana sannan mu tattauna. Sannan ya na daraja shugaban kasa Muhammadu Buhari.” Inji Uzo Kalu.
Discussion about this post