Rundunar ‘yan sandan jihar Borno ta kama gungun ‘yan kungiyar matsafa da suka shahara da yin gunduwa-gunduwa da jikin mutane a jihar suna siyar wa.
Kwamishinan ‘yan sandan jihar Abdu Umar da ya sanar da haka ranar Juma’a ya ce rundunar ta kama gungun matsafan wanda aka fi sani da ‘Karangiya’ ranar 16 ga Disamba 2022.
Umar ya ce kungiyar matsafan sun rika kama mutane suna yin gunduwa-gunduwa da su inda a kwanakin baya ma sun kwakule idanun wani mutum da suka kama a ofishin aikawa da wasiku wato ‘Post Office’.
“Akwai Kuma lokacin da aka tsinci gawar wata mata da kungiyar suka kashe sannan suka cire wasu bangarorin jikinta kuma suka jefar da ganganr jikin a wani tafki.
“A dalilin haka ya sa rundunar ta gudanar da bincike domin gano mutanen da suka kashe matar.
Umar ya ce a ranar 16 ga Disamba 2022 kungiyar matsafa ta kai wa wani Mohammed Bukar mai shekara 18 daga kauyen Shuwari dake Maiduguri da abokinsa hari.
“Kungiyar ta afka wa Mohammed da abokinsa yayin da suke hanyar karbo wayar Mohammed daga wurin caji.
“Yayin da kungiyar ke lakadawa Mohammed duka abokinsa ya gudu sannan wani cikin ‘yan kungiyar mai suna Ali Bukar ya zaro wuka zai yanki Mohammed a kai amma sai ya kare kansa.
“Daga nan wani dan kungiyar ya zaro adda ya sari Mohammed a hannu.
“Mohammed ya shigar da kara a ofishin ‘yan sandan dake Jere.
Umar ya ce bayan Mohammed ya shigar da karan ne rundunsr ‘yan sandan ta kama Ali Bukar tare da wasu ‘yan kungiyar guda 8.
Ya ce za a Kai su da zaran kotu ta kammala gudanar da bincike.
Discussion about this post