Gwamnatin Tarayya ta bayar da sanarwar cewa an yi mummunar asarar rayukan mutane 500, tare da lalata gidaje fiye da 90,000 a faɗin ƙasar nan, sanadiyyar ambaliya.
Ambaliyar wadda ta shafi jihohi 31, ta fi tsanani a jihohin Jigawa, Kogi, Kebbi da Bayelsa.
Babban Sakataren Ma’aikatar Jinƙai, Agaji da Inganta Rayuwar Marasa Galihu, Nasir Sani-Gwarzo ne ya tabbatar da waɗannan adadin alƙaluma, cikin ganawar da ya yi da manema labarai a ranar Talata, Abuja.
“Aƙalla fiye da mutum miliyan ɗaya ne ambaliya ta kora daga gidajen su, aka yi asarar rayuka 500, tare da samun wasu mutum 1,546 da su ka ji raunuka.
“Ambaliya ta yi wa gidaje 44,099 ɓarna, yayin da ta lalata wasu gidajen har 45, 249 baki ɗayan su.
“Aƙalla ruwa ya lalata amfanin gona a gonaki 76,168, yayin da wasu gonakin su ka lalace gaba ɗaya har guda 70,566 kwata-kwata.”
Sani ya ƙara da cewa masana da jami’an bincike sun tabbatar da cewa ambaliyar ta 2022 ta kai munin ta 2012.
Ya ce tuni Hukumar Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) ta fara shirin raba kayan tallafi da agaji, wanda ya ce sama da mutane 315,000 ne za su ci moriyar agajin.
Discussion about this post