An samu raguwa a yawan mutanen da ‘yan bindiga suka kashe a kasar nan inda a makon jiya mutum 27 ne suka kashe.
Daga cikin mutanen da aka kashe 22 farin hula ne, ‘yan sanda 4, sibul difens daya.
Kai wa jerin gwanon motocin shugaban ƙasa Muhammadu Buhari a Daura jihar Katsina da Kai wa gidan yarin Kuje a Abuja na daga cikin hare-haren da ‘yan bindiga suka yi a makon jiya.
Kudu maso Gabas
A ranar Lahadin da ya gabata a jihar Abia mutane sun banka wa wasu mutum uku da ake zargi ‘yan fashi da makami a karamar hukumar Aba.
Barayin sun saba yi wa masu sana’ar POS fashi musamman wadanda ke kauyen Abayi dake hanyar Aba zuwa Owerri a Aba.
Bayan haka a ranar Litinin mutane sun cinna wa wasu mutane biyu wuta a bisa zargin su matsafa ne.
Kudu maso Yamma
A kauyen Igoba dake karamar hukumar Akure ta Arewa a jihar Ondo ‘yan bindiga sun kashe wani mai gadin gidan manfetur mai suna Sunday ranar Litini.
Maharan sun kuma cinna wa gidan man wuta sannan suka tafi.
Arewa ta Tsakiya
Akalla mutum 12 ne suka mutu a wani mummunar rikicin da aka yi tsakanin ‘yan bindiga da ‘yan kungiyar sa kai a jihar Filato.
Mazauna kauyen Zak dake karamar hukumar Wase sun ce maharan sun afka kauyen su domin kashe kowa a kauyen.
A jihar Kwara ‘yan bindiga sun kashe wani dan sanda Adebayo Adeforiti sannan suka yi garkuwa da dan kasan Chana dake aiki a Kamfanin CGC dake hanyar Shao/Oloru.
Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Okasanmi Ajayi ya ce hakan ya faru ranar Lahadin da ya gabata.
Discussion about this post