Jami’an kiwon lafiya sun bayyana cewa wata cuta da ake zaton cutar sankarau ce ta kashe yara 65 a kananan hukumomi 14 a jihar Jigawa.
Wakilin PREMIUM TIMES da ya tattauna da mazauna da jami’an lafiya a ziyarar da ya kai wasu kananan hukumomin da cutar ta barke sun bayyana cewa mafi yawan yaran da suka kamu da cutar sun fara cewa suna jin ciwon Kai, zazzabi da rashin iya tafiya.
Kananan hukumomin Gumel, Babura da Sule-Tankarkar na daga cikin kananan hukumomin da wakilin mu ya ziyarta ranar Laraba.
Mai unguwan kauyen Dungundun dake karamar hukumar Sule-Tankarkar Alkasim Yakubu ya ce cutar ta kashe yara 19 sannan wasu yaran da dama na fama da wani nakasa a jikinsu a dalilin cutar.
Yakubu ya ce a dalilin bullowar cutar mutane da dama sun yi wa Dungundun Kaura domin guje wa kamuwa da cutar.
Ya ce cutar ta yi sanadiyyar rayukan wasu tsofaffi biyu a kauyen.
“Cutar ya fara bulla a kauyen a tsakiyar watan da ya gabata inda yaran da suka kamu da cutar ke mutuwa a cikin sa’o’i 12.
“Abin takaicin shine yadda babu asibiti a kauyen inda dole muke kai wadanda suka kamu da cutar cibiyar kiwon lafiya na matakin farko a karamar hukumar Danladin Gumel.
Yakubu ya koka da yadda gwamnati ta yi watsi da kawo musu dauki musamman kauyukan da cutar ta barke.
“Tun da wani jami’in karamar hukuma ya aiko wa mutane maganin da ake zubawa a ruwan sha ba mu sake samun wani dauki daga wajen gwamnati ba.
Yakubu ya ce da dama daga cikin yaran da suka kamu da cutar sun mutu ne a gida sannan wadanda suka wsrke na fama da nakasa a jikinsu.
Ya ce wata Kungiya mai zaman kanta ‘Save the Children’ na taimakawa wajen kula da yaran da suka kamu da cutar.
“Kungiyar ta taimaka wajen wayar da kan mutane game da cutar, mahimmancin wanke hannu da ruwa da sabulu, tsaftace muhalli da illan yin bahaya a waje.
Yakubu ya Kuma lissafo kauyuka da yawan yara da suka mutu a kowace kauye kamar haka; Abdulfatahu kanta, 3, Sha’awa kanta, 3, Gambo Alka, 7, Umaru Audu, 2, Shu’aibu Abba, 3, Sama’ila Magaji, 10, Rabilu Abdulaziz, 15 da Muktaka Muhammadu, 20.
Saura sun hada da Zirkifilu Gambo, 8, Shahida Hassan,12, Shamsi Lawalli, 25, Habiba Yahaya,3, Habu Babandi, 3, Ashafa Maigari, 5, Ummah Miko, 4, Ya’u Jinaidu, 9, Yunusa Haruna, 4, Habi Lawan, 80 da Sabo Awe, 80.
Dakacen kauyen Mele dake karamar hukumar Gumel Yusuf Ahmad ya ce akalla mutum 21 sun mutu a sanadiyyar kamuwa da cutar a kauyen.
Ahmad ya ce jami’an lafiya na karamar hukumar sun taimaka wajen kula da mutanen da suka kamu da cutar inda a yanzu haka mutum 30 sun warke.
Dagacen kauyen Gidan Maja Akilu Dawaki a karamar hukumar Bubara ya ce cutar ta yadu zuwa kauyuka da dama a karamar hukumar.
Dawaki ya ce kauyukan Kanya Arewa Kanya Yamma na daga cikin kauyukan da suka fi fama da cutar.
“Mun sanar wa jami’an kiwon lafiya na karamar hukumar inda suke taimakawa wajen wayar da kan mutane game da cutar.
“Cutar ta yi ajalin mutum 19 a kauyen sannan mutanen da suka mutu a dalilin cutar sun mutu ne a gida.
Ya ce cutar ya fi yaduwa a Gidan Maja inda a kauyen yara 8 ne suka mutu.
Sauran kauyukan da cutar ta bullo a karamar hukumar Bubara sun hada da Jigawa, Babura Kofar Yamma, Kwando, Insha Ruwa, Gidan Ibira da Alfatiha.
Wani magidanci Ado Kanta wanda ya rasa ‘ya’yan sa biyu a dalilin cutar ya ce dansa Abdulfatahu dake fa shekaru 3 ne ya fara kamuwa da cutar yana amai da gudawa inda cikin ɗan ƙanƙanin lokaci ya rasu.
Kanta ya ce daga nan sai ‘yarsa Sha’awa mai shekara uku ta rasu a babban asibitin Gumel bayan cibiyar lafiya na Gumel ta ki karban yarinyar.
“Cutar ta ci gaba da yaduwa ba tare da gwamnati ta kawo wa mutane dauki ba inda wani Limami ya bada shawarar a tashi da addu’o’i.
Shugaban masu gudanar da binciken kan bullowar cututtuka na jihar Sama’ila Mahmud ya ce ana zargin cewa mutum 257 ne suka kamu da cutar daga kananan hukumomi 14 a jihar.
Mahmud ya ce sakamakon gwajin da aka yi ya nuna cewa mutum 10 ne suka kamu da cutar.
Ya ce zuwa yanzu gwamnati ta hada hannu da kungiyar ‘ Save the Child’s domin dakile yaduwar cutar.
Gwamnati ta Kuma dauki nauyin wayar da kan mutane musamman yara kanana domin kare kansu daga kamuwa da cutar.
Discussion about this post