Rikicin zargin wulaƙanta Sarkin Kano Aminu Ado-Bayero da ake tsakanin Masarautar Kano da kamfanin zirga-zirgar jiragen sama na Air Peace, a yanzu ya ɗauki sabon salo tun a ranar Asabar, lokacin da Isa Bayero ya bai wa Air Peace wa’adin sa’o’i 72 cewa ya gaggauta neman afuwa daga wurin Sarkin Kano.
Premium Times Hausa ta kawo dalilan da su ka harzuƙa Masarautar Kano neman afuwar Air Peace a cikin kwanaki uku.
Ɗaya daga cikin ‘ya’yan Sarki a Kano, mai suna Isa Bayero, ya bai wa kamfanin zirga-zirgar jiragen sama na Air Peace wa’adin sa’o’i 72 cewa su nemi afuwar tozarta Sarkin Kano Aminu Ado-Bayero da jirgin ya yi, har ya haddasa wa sarkin da tawagar sa ɓata lokaci.
Bayero wanda kawun sarki ne, ya bayyana wannan sanarwa ce a ranar Asabar, yayin da ya ke magana da wasu manema labarai a Kano, ciki har da wakilin PREMIUM TIMES.
Ya ƙara da cewa tilas kuma kamfanin Air Peace ya amsa laifin da ya yi na rashin tashi lokacin da aka ƙa’ide masa, wanda ya ce hakan ya haddasa ɓata lokaci da jinkiri ga Sarkin Kano, wanda aka bar shi a tashar jirage ta Legas zaman dirshan ɗin jirgi.
Tun da farko dama Bayero ya rubuta takardar koke da ƙorafin laifin da ya ke iƙirarin Air Peace sun yi wa Sarki Aminu ga Hukumar Kula da Sararin Samaniyar Najeriya (NCAA) domin ta yi hukuncin da ya dace a kan kamfanin.
Isa, wanda aka fi sani da Isa Pilot, ya ce Air Peace ya haddasa masu ɓata lokacin awa ɗaya a tafiyar dawowar su daga Banjul a Gambiza zuwa Legas. Sannan kuma ya ce an hana ‘yan tawagar sarki shiga jirgin da zai tafi Kano.
Isa ya ce ‘yan rakiyar Sarki sun isa Legas minti 30 kafin lokacin tashin jirgi.
Ƙorafin Isa na ƙunshe iƙirarin cewa ya kira Shugaban Air Peace Allen Onyema, cewa ya sa a jinkirtar da jirgin da zai tafi Legas da safe saboda batun Banjul.
“Amma sai ya ƙi yin hakan, ya ce ba zai yi haka ba. To ni a ƙashin kai na na ɗauki abin da aka yi a matsayin cin fuska ha Mai Martaba Sarkin Kano da mutanen Kano baki ɗayan su.” Inji Isa Bayero a cikin wasiƙar ƙorafin.
Ya shaida wa manema labarai cewa zai ci gaba da yin magana har sai lokacin da Allen Onyema ya bai wa Sarkin Kano haƙuri.
Bayero ya ƙaryata iƙirarin da Air Peace ya yi, inda ya ce sun yi wa sarkin tayin wani jirgin daban, wanda zai ɗauke Sarki da tawagar sa daga Abuja zuwa Kano, cewa ƙarya ce ba a yi hakan ba.
“Ni da kai na na nemi alfarmar Sarki ya bi wanan jirgi daga Abuja zuwa Kano, amma Sir Peace su ka ce min ya cika.” Inji Isa Bayero.
Ya ce a ƙarshe ma daina ɗaukar kiran lambar sa Air Peace ya yi.
“Mun rigaya mun sayi tikitin jirgin, don haka ban ga yadda za a yi su tashi su bar mu ba. Wannan cin mutuncin Sarki da al’ummar Kano ne baki ɗaya.
“Saboda haka ina bai wa Air Peace wa’adin sa’o’i 72 ya bada haƙuri ga Sarki a cikin wasu jaridun ƙasar nan masu fitowa kowace rana. Idan ba haka ba kuma, za mu ƙara gaba har sai mun dangana inda za a gyara wa Air Peace zama.” Inji Isa Pilot, wanda ya yi kurarin cewa shi ma tsohon diraban jirgin sama ne, har ma ya taɓa tuƙa shugabanni biyar.
A ƙarshe ya nuna bai damu ba idan Air Peace ya daina zuwa Kano, domin a cewar sa, tun kafin a kafa Sir Peace Kanawa ke zirga-zirga a jiragen sama.
Raddin Air Peace A Kan Masarautar Kano:
A raddin Air Peace, kamfanin ya ce, “ta yaya Isa Bayero zai kira mahukuntan Air Peace su tsaida jirgin ya yi latti, bayan har an gama shiga, an kulle ƙofa, kuma jirgin ya fara tafiya, a lokacin kuma Sarkin Kano da ‘yan rakiyar sa takwas har da Isa Bayero su na filin jirgin saman Lagos, bayan saukar su daga Banjul, Gambiya? Ta yaya za a tsaya kuma jiran su?”
Air Peace sun bayar da wata hujja cewa Isa Bayero ya kira Onyema, Shugaban Air Peace misalin ƙarfe 5:52 na asubahi, lokacin da ya ke tsakiyar barcin sa.
Air Peace ya ce kenan Bayero ne ma ya tashi Onyema daga barci.
“Yayin da ya ga lambar Isa Bayero ce, sai ya amsa kiran, ya ce shi da Sarkin Kano sun iso filin jirgin jirgin sama na Legas daga Banjul, birnin Gambiya, kuma Kano za su zarce a lokacin.”
“Ya sanar da Shugaban Air Peace ya da jirgin na Legas zuwa Kano ya yi latti zuwa ƙarfe 6:15, domin shi da Sarki da sauran mutum takwas su samu shiga. Don haka ba wai Onyema ya ƙi sauraren sa ba ne.
“Daga nan ya ce da Isa Bayero ya ba shi ‘yan mintina don ya kira filin jirgi ya ji halin da jirgin wanda zai tashi daga Legas zuwa Kano da sassafen ranar ya ke ciki. Daga nan kuma ya kira ni, don ya ji halin da ake ciki.”
“Ni ne Babban Jami’in Kula da Jigilar Fasinjoji na Air Peace. Nan da nan mu ka kira, aka ce mana ai jirgin ma har ya gama lodi, ya fara gudu a ƙasa.”
Yayin da wasu ke goyon bayan Air Peace, wasu kuma goyon bayan Masarautar Kano su ke yi, saboda wulaƙancin da su ke ganin an yi wa Sarkin Kano sukutum, an ƙi jiran sa.
A cikin 2019, rahoton da NCAA ta fitar ya nuna an samu rahotonnin ɓacewar kaya da kuma lattin kayan fasinjoji har sau 41,968 a Najeriya.
Sannan kuma an samu tashin jirage sau 65,401, wanda fiye da rabin su, wato 37,510 duk a makare su ka tashi, yayin da aka soke tashin jirage har sau 356.
Tambayoyi Ga Air Peace:
Isa Bayero ya yi iƙirarin cewa Air Peace ya nemi su Sarkin Kano su biya kuɗin harajin ƙin hawan wancan jirgi da ba su samar yi ba, ya yin da su ka je su nemi shiga jirgin ƙarfe 7 na safe. Haka Isa ya yi wa NCAA ƙorafi.
Sai dai yayin da Air Peace ke kare kan sa gaban taron manema labarai, bai yi magana a kan wannan batun ba.
Shi ma Kakakin Air Peace Stanley Olisa, bai yi magana kan wannan batun ba a lokacin da yake magana da PREMIUM TIMES ta wayar tarho.
Masana harkar jiragen sama irin su John Ojikutu, sun ce ba daidai ba ne jirgi ya yi shirin tashi kuma ya tsaya saboda jiran wani fasinja.
Sai dai kuma ya ce tun farko, tunda Air Peace ya ji cewa wani babban mutum ne, to sai su bada haƙuri kawai, a wuce wurin.
Wasu kuma na cewa ya kamata kawai Masauntar Kano ta maka Air Peace kotu.
Discussion about this post