Ma’aikatar Lafiya ta gargaɗi mahajjatan Najeriya na bana da su nisanta kansu daga cin ganda da nama daji da ake kira ‘Bush Meat’
Hakan ya biyo bayan bullowar cutar Anthrax a wasu kasashe da ke makwabtaka da Najeriya da ya ke dada yaduwa a sauran kasashen.
Kwamishinan lafiya na hukumar NAHCON Saidu Dumbulwa ya fidda wannan sanarwar ranar Laraba.
Dumbulwa ya ce cutar Anthrax ta bullo a kasashen Ghana, Burkina Faso da Togo.
Ya ce alamun cutar sun hada da zazzabi, tari da ciwon jiki.
“A dalilin haka muke gargaɗin mahajjata da su nisanta kansu daga cin ganda, nama ko madaran da aka shigo da su daga waɗannan kasashe
Idan ba a manta ba PREMIUM TIMES HAUSA ta buga labarin cewa gwamnatin Najeriya ta gargadi mutane su daina cin naman daji da ganda domin guje wa kamuwa da cutar Anthrax.
Likitocin dabobbi sun bayyana cewa yi wa dabbobi allurar rigakafin cutar na daga cikin hanyoyin dakile yaduwar cutar.
Za a iya samun maganin yin allurar rigakafin a babban asibitin dabbobi na kasa dake Vom jihar Filato.
Likitocin sun ce a killace dabbobin da suka kamu da wannan cuta domin gudun yadawa a tsakanin wasu dabbobin.
Sun kuma ce dabbobin da basu kamu da cutar ba ne kawai za a iya yi wa allurar rigakafin cutar.
Discussion about this post