Ma’aikatan kiwon lafiya na asibitin kwakwalwa dake jihar Enugu sun dage kan ci gaba da yajin aiki da suke yi.
Ma’aikatan sun ce baza su hakura ba sai gwamnati ta amince ta biya musu bukatun su tukuna.
A yanzu haka ma’aikatan sun kai tsawon kwanaki 13 suna yajin aiki kenan.