Jagoran Alƙalan Kotun Ɗaukaka Ƙararrakin Zaɓen Shugaban Ƙasa, ya ce kotu ba za ta karɓi shaidar ƙwararriyar masaniyar logar yanar gizo da manhaja, wadda ɗan takarar shugaban ƙasa na LP Peter Obi ya gabatar a baya ba.
Ya bayyana cewa lauyoyin Tinubu ne su ka bayar da hujjar cewa masanin kuma injiniyar mai suna Mpeh Ogar ba ‘yar-ba-ruwan-mu ba ce, ‘yar jam’iyyar LP, wanda kotu ta ce ta tabbatar har ma takara ta taɓa tsayawa a ƙarƙashin LP.
Tsammani ya ce kotu ba za ta amshi shaidar ta ba, saboda ɗan ɓangaranci ne. A irin wannan shaida kuwa a cewar kotu, ana ɗauko ƙwararren da ba shi a wata alaƙa, nasaba ko kusanci da jam’iyya ne ko ɗan takarar da ya shigar da ƙara.
Discussion about this post