• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Uba Sani ya yi alhini da ta’aziyyar kisan dandazon ƴan maulidi a Kaduna, ya umarci a gudanar da bincike

    Uba Sani ya yi alhini da ta’aziyyar kisan dandazon ƴan maulidi a Kaduna, ya umarci a gudanar da bincike

    Hukumar Tashoshin Jiragen Ruwa ta soke dadaddiyar kwangilar da ta ke yi da Intels, kamfanin Atiku

    Hukumar Tashoshin Ruwa ta maida wa kamfanin Intels aikin karɓar haraji a tashoshin ruwan Najeriya

    ‘Yan sanda sun damke faston da ake zargin yayi wa ‘yar shekara 19 fyade

    GARKUWA DA MUTANE: Kotu ta yanke wa Sarkin Fulani, Usman daurin rai da rai

    FATA NAGARI LAMIRI: Tinubu ya raba laƙanin yadda ƙarfin tattalin arzikin Najeriya zai kai dala tiriliyan 1 nan da shekaru 10

    FATA NAGARI LAMIRI: Tinubu ya raba laƙanin yadda ƙarfin tattalin arzikin Najeriya zai kai dala tiriliyan 1 nan da shekaru 10

    KASAFIN NAIRA TIRILIYAN 27.5 NA 2024: ‘Za a ciwo bashin Naira tiriliyan 8.83 domin cike giɓin haƙoran kasafin’ – Tinubu

    KASAFIN NAIRA TIRILIYAN 27.5 NA 2024: ‘Za a ciwo bashin Naira tiriliyan 8.83 domin cike giɓin haƙoran kasafin’ – Tinubu

    KASAFIN 2024: Tilas mu yi aiki da kasafin kuɗi tare, domin yi wa ‘yan Najeriya aikin da za su yi alfahari da mu da ƙasar mu

    KASAFIN 2024: Tilas mu yi aiki da kasafin kuɗi tare, domin yi wa ‘yan Najeriya aikin da za su yi alfahari da mu da ƙasar mu

    Hukumar NDLEA ta kama tan 15.7 na haramtattun kwayoyi a jihar Kano

    Hukumar NDLEA ta kama tan 15.7 na haramtattun kwayoyi a jihar Kano

    RA’AYIN PREMIUM TIMES: KISAN GILLAR SOJOJIN NAJERIYA: A gaggauta hukunta masu ɗaukar nauyin ‘yan ta’adda, domin a raya Sojojin Najeriya

    Kotu ta bada belin maza biyu da suka jibgi wani tsoho bisa zargin ya sace musu gaba

    Ƴan siyasan Najeriya na naɗa makusantan su cikin hukumar zaɓe don su rika samun yadda suke so  – Jega

    Jega ya nemi Tinubu ya tsira da mutuncin sa, ta hanyar sauke ‘yan APC da ya naɗa kwamishinonin zaɓe

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    Saura ƙiris Liverpool ta zubda abin faɗi a wasan Premier League na ranar Lahadi

    Saura ƙiris Liverpool ta zubda abin faɗi a wasan Premier League na ranar Lahadi

    MESSIN DAI: Leo Messi ya lashe kyautar ɗan kwallon duniya ta Ballon d’Or a karo na takwas

    MESSIN DAI: Leo Messi ya lashe kyautar ɗan kwallon duniya ta Ballon d’Or a karo na takwas

    Hukumar CAF za ta binciki yadda mahaifiyar ɗan wasa ta mutu cikin 1986, shi kuma ya ce atabau cikin 1990 ta haife shi

    A karo na Uku, Moroko za ta ɗauki baƙuncin gasar cin kofin kwallon ƙafa na nahiyar Afrika a Janairun 2025

    NFF ta sake nada Chris Danjuma a matsayin kocin Falconets

    NFF ta sake nada Chris Danjuma a matsayin kocin Falconets

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    BIDIYO: Dalilin da ya sa na ziyarci Tinubu – Uba Sani

    BIDIYO: Dalilin da ya sa na ziyarci Tinubu – Uba Sani

    BIDIYO: Tinubu masoyin ‘Yan jarida ne – Idris

    BIDIYO: Tinubu masoyin ‘Yan jarida ne – Idris

    Timipre-Sylva

    TANGARƊA A APC: Kotu ta hana Sylva, tsohon Ministan Fetur tsayawa takarar zaɓen gwamnan Bayelsa

    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    JERIN SUNAYE: Jami’o’i 51 da ba za su dauki dalibin da ya ci kasa da maki 180 a jarabawar JAMB ba

    TSARIN BAI WA ƊALIBAI RAMCE: Abubuwan da suka wajaba ɗalibai da iyaye su sani

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Uba Sani ya yi alhini da ta’aziyyar kisan dandazon ƴan maulidi a Kaduna, ya umarci a gudanar da bincike

    Uba Sani ya yi alhini da ta’aziyyar kisan dandazon ƴan maulidi a Kaduna, ya umarci a gudanar da bincike

    Hukumar Tashoshin Jiragen Ruwa ta soke dadaddiyar kwangilar da ta ke yi da Intels, kamfanin Atiku

    Hukumar Tashoshin Ruwa ta maida wa kamfanin Intels aikin karɓar haraji a tashoshin ruwan Najeriya

    ‘Yan sanda sun damke faston da ake zargin yayi wa ‘yar shekara 19 fyade

    GARKUWA DA MUTANE: Kotu ta yanke wa Sarkin Fulani, Usman daurin rai da rai

    FATA NAGARI LAMIRI: Tinubu ya raba laƙanin yadda ƙarfin tattalin arzikin Najeriya zai kai dala tiriliyan 1 nan da shekaru 10

    FATA NAGARI LAMIRI: Tinubu ya raba laƙanin yadda ƙarfin tattalin arzikin Najeriya zai kai dala tiriliyan 1 nan da shekaru 10

    KASAFIN NAIRA TIRILIYAN 27.5 NA 2024: ‘Za a ciwo bashin Naira tiriliyan 8.83 domin cike giɓin haƙoran kasafin’ – Tinubu

    KASAFIN NAIRA TIRILIYAN 27.5 NA 2024: ‘Za a ciwo bashin Naira tiriliyan 8.83 domin cike giɓin haƙoran kasafin’ – Tinubu

    KASAFIN 2024: Tilas mu yi aiki da kasafin kuɗi tare, domin yi wa ‘yan Najeriya aikin da za su yi alfahari da mu da ƙasar mu

    KASAFIN 2024: Tilas mu yi aiki da kasafin kuɗi tare, domin yi wa ‘yan Najeriya aikin da za su yi alfahari da mu da ƙasar mu

    Hukumar NDLEA ta kama tan 15.7 na haramtattun kwayoyi a jihar Kano

    Hukumar NDLEA ta kama tan 15.7 na haramtattun kwayoyi a jihar Kano

    RA’AYIN PREMIUM TIMES: KISAN GILLAR SOJOJIN NAJERIYA: A gaggauta hukunta masu ɗaukar nauyin ‘yan ta’adda, domin a raya Sojojin Najeriya

    Kotu ta bada belin maza biyu da suka jibgi wani tsoho bisa zargin ya sace musu gaba

    Ƴan siyasan Najeriya na naɗa makusantan su cikin hukumar zaɓe don su rika samun yadda suke so  – Jega

    Jega ya nemi Tinubu ya tsira da mutuncin sa, ta hanyar sauke ‘yan APC da ya naɗa kwamishinonin zaɓe

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    Saura ƙiris Liverpool ta zubda abin faɗi a wasan Premier League na ranar Lahadi

    Saura ƙiris Liverpool ta zubda abin faɗi a wasan Premier League na ranar Lahadi

    MESSIN DAI: Leo Messi ya lashe kyautar ɗan kwallon duniya ta Ballon d’Or a karo na takwas

    MESSIN DAI: Leo Messi ya lashe kyautar ɗan kwallon duniya ta Ballon d’Or a karo na takwas

    Hukumar CAF za ta binciki yadda mahaifiyar ɗan wasa ta mutu cikin 1986, shi kuma ya ce atabau cikin 1990 ta haife shi

    A karo na Uku, Moroko za ta ɗauki baƙuncin gasar cin kofin kwallon ƙafa na nahiyar Afrika a Janairun 2025

    NFF ta sake nada Chris Danjuma a matsayin kocin Falconets

    NFF ta sake nada Chris Danjuma a matsayin kocin Falconets

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    BIDIYO: Dalilin da ya sa na ziyarci Tinubu – Uba Sani

    BIDIYO: Dalilin da ya sa na ziyarci Tinubu – Uba Sani

    BIDIYO: Tinubu masoyin ‘Yan jarida ne – Idris

    BIDIYO: Tinubu masoyin ‘Yan jarida ne – Idris

    Timipre-Sylva

    TANGARƊA A APC: Kotu ta hana Sylva, tsohon Ministan Fetur tsayawa takarar zaɓen gwamnan Bayelsa

    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    JERIN SUNAYE: Jami’o’i 51 da ba za su dauki dalibin da ya ci kasa da maki 180 a jarabawar JAMB ba

    TSARIN BAI WA ƊALIBAI RAMCE: Abubuwan da suka wajaba ɗalibai da iyaye su sani

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

AREWA A HANNUN ‘YAN BINDIGA: Yadda ‘yan bindiga suka riƙa jidar ɗaliban Jami’ar Gusau, su na nausawa da su cikin surƙuƙin Dajin Kuyambana

Ashafa MurnaibyAshafa Murnai
September 27, 2023
in Babban Labari
0
AREWA A HANNUN ‘YAN BINDIGA: Yadda ‘yan bindiga suka riƙa jidar ɗaliban Jami’ar Gusau, su na nausawa da su cikin surƙuƙin Dajin Kuyambana

Tabbatattun bayanai sun nuna yadda ‘yan bindigar da suka kutsa gidajen kwanan ɗaliban Jami’ar Gusau suka kwashi mata, suka nausa da su cikin Dajin Kuyambana.

‘Yan ta’addar sun afka gidajen kwanan ɗalibai mata har uku a Sabon Gida, kusa da Gusau, babban birnin Jihar Zamfara, suka jidi mata 24 kan babura, a ranar Juma’a.

Zuwa ranar Talata dai gamayyar zaratan jami’an sojoji, ‘yan sanda da sauran jami’ai sun ceto 13 a arangama biyu da suka yi.

Mazauna yankin Sabon Gida ciki har da basaraken gargajiyar yankin, waɗanda suka ga yadda lamarin ya faru, sun shaida wa PREMIUM TIMES cewa bayan ‘yan bindiga sun kai farmakin, sun riƙa kwasar matan su na darzazawa dajin Ɗansadau a cikin Ƙaramar Hukumar Maru, a tsakanin ranakun Juma’a da Litinin.

Sun riƙa yin walankeluwa da matan kan babura a yankin Dajin Kuyambana.

Wannan jarida ta gano cewa ‘yan bindiga da matan da suka kwashe sun kwana a cikin masallaci a ranakun Asabar da Lahadi, a wasu ƙauyuka biyu na yankin Ɗansadau.

Mazauna yankin sun tabbatar da cewa ranar Litinin kuma ‘yan bindiga tare da matan da suka kwashe sun isa Dajin Madada, daji mafi wawakeken faɗi a Gandun Dajin Kuyambana.

Dajin Kuyambana: Gandun Dajin Gwamna A Hannun ‘Yan Bindiga:

An tabbatar da Dajin Kuyambana a ƙarƙashin ikon ‘yan bindiga ya ke, waɗanda ke ƙarƙashin gogarma Ali Kachalla da Dogo Giɗe. An kuma haƙƙaƙe cewa Ali Kachalla da Dogo Giɗe ne suka tura aka kwaso matan da ƙarfin muggan makamai.

‘Yan Bindiga Sun Yada Zango, Suka Kwana Cikin Masallaci:

“Bayan sun kwashi matan daga gidajen kwanan ɗaliban jami’a uku, sun zarce Gajeren Ƙauye da ke kilomita uku kusa da Ɗansadau. A Gajeren Ƙauye suka gwamutsu a cikin masallaci ɗaya suka kwana. Ranar Lahadi kuma suka nausa ƙauyen Kukar Magu da ke tazarar kilomita takwas daga garin Ɗansadau.

Sun isa sansanin su cikin Dajin Madada safiyar Litinin, inda suka jera wa gogarman su Ali Kachalla matan da suka kamo daga Jami’ar Gusau.”

Wani mazaunin yankin da ya roƙi mu ɓoye sunan sa ne ya tabbatar da haka ga PREMIUM TIMES.

Kakakin Yaɗa Labaran ‘Yan Sandan Jihar Zamfara, Yazeed Abubakar ya ce ‘yan sanda ne ya kamata a sanar wa da irin wannan labari da wuri-wuri, domin su kai ɗaukin ceto.

Ya ce jami’an tsaro na kan ƙoƙarin cewa waɗanda ke hannun ‘yan bindiga ɗin.

“Muna roƙon jama’a su riƙa bai wa jami’an tsaro irin waɗannan bayanai cikin hanzari, domin su kai ɗauki da gaggawa.” Inji Kakakin ‘Yan Sandan Zamfara.

Yadda Kachalla Da Dogo Giɗe Suka Kafa Ƙaƙƙarfar Dabar Tara Kuɗaɗen Fansa:

An haƙƙaƙe cewa Ali Kachalla da Dogo Giɗe sun fi sauran ‘yan bindiga kafa ƙaƙƙarfar dabar tara kuɗaɗen fansa a Arewa maso Gabas da Arewa ta Tsakiya.

A na su tsarin garkuwa da mutane, sun haramta wa yaran su kai farmaki cikin ƙauyukan kewayen Dajin Kuyambana. Sun fi maida hankali wajen kai hare-hare a makarantun gwamnati, kama jami’an gwamnati, ko hari a cibiyoyin gwamnati. Sukan tare matafiya su yi garkuwa da su, musamman waɗanda ke cikin motocin gwamnati.

Irin wannan salon garkuwa da su ke yi, sai su kuma mazauna ƙauyukan da ke kusa da dajin ke jin daɗin maƙauyaka da irin su Kachalla da Dogo Giɗe, saboda ba su kai masu hare-hare, kuma babu wasu masu garkuwar da za su iya tsallakawa daga wasu dazuka su kai masu hari.

Mazauna yankunan karkara da dama sun ce an samu sauƙin kai hare-hare ne a yankin Ɗansadau sakamakon umarnin da su Dogo Giɗe suka yi cewa a daina kai wa ƙauyuka farmaki.

Sun daina kai hare-hare, sai dai su kan tura ‘jakadun su’ cikin Ɗansadau domin a yi sulhun sasanta rikici. Idan kuma wasu ‘yan bindiga su ka yi gangancin kai wa mazauna yankin hari, to su Dogo Giɗe kan sa a ladabtar da su.

Kada a manta, su Dogo Giɗe ne suka kwashi ‘yara ‘yan makaranta 136 daga Islamiyyar Salihu Tanko a garin Tegina, cikin Ƙaramar Hukumar Rafi, a Jihar Neja, a ranar 39 ga Mayu, 2021.

Su ne kuma su ka jidi ɗalibai da malaman Kwalejin Gwamnatin Tarayya ta Yawuri, a Jihar Kebbi, cikin watan Yuni, 2021.

Su ne kuma a baya su ka riƙa kai wa makarantun sakandare hare-hare a Katsina da Kaduna, har sai da ta kai aka rufe dukkan makarantun da ake tsoron za a iya kai wa farmaki.

Majiya ta ce dabar Kachalla da ta Dogo Giɗe kan karkasa waɗanda suka kama a tsakanin su, daga nan sai su riƙa yin jinga da gwamnati ko iyayen waɗanda suka kama, su yanka farashi, ana tayawa, su na cewa albarka.

Dajin Kuyambana da ke cikin Ƙaramar Hukumar Ɗansadau, ya mamaye murabba’in sikwaya kilomita 492 a Jihar Zamfara. Yanki ne mai albarkar noma da kiwo.

A baya PREMIUM TIMES Hausa ta buga labarin yadda ‘yan bindiga suka ragargaji Sansanin Zaratan Sojoji a ƙauyen Matunji da ke ƙarƙashin yankin Ɗansadau. A farmakin sai da suka kashe Sojojin Sama 9, ‘yan sanda 2, da soja 1.

A dajin Ɗansadau, ‘yan bindiga na mamaye ƙauyukan da dabu jami’an tsaro, su tsige dagaci ko mai unguwa, su ƙaƙaba wa jama’a harajin ladar kula da tsaron su. Wanda ba ya iya tsayawa kuwa, su ce ya bar garin, ya ƙara gaba.

Tags: BanditsGusauNewsPREMIUM TIMESSojojiZamfara
Previous Post

Yadda zan tsayar da taɓarɓarewar darajar naira – Cardoso, sabon Gwamnan CBN

Next Post

UNICEF ta saka Almajirai sama da 20,000 cikin rajistar tsarin agaza wa marasa karfi a Katsina

Ashafa Murnai

Ashafa Murnai

Next Post
Almajirai

UNICEF ta saka Almajirai sama da 20,000 cikin rajistar tsarin agaza wa marasa karfi a Katsina

Discussion about this post

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • Ƴan sanda sun kashe ƴan bindiga biyu a jihar Adamawa
  • ZANGA-ZANGAR ƊALIBAI: Jami’ar ATBU ta dakatar da karatu na tsawon mako guda
  • Uba Sani ya yi alhini da ta’aziyyar kisan dandazon ƴan maulidi a Kaduna, ya umarci a gudanar da bincike
  • Kasafin 2024 ya bada fifiko ne wajen jaddada Ajandar Saisaita Najeriya – Idris
  • SHIRIN BUNKASA ILMI: Jarabawar gwaji ba za ta hana mu ɗauki dukkan malaman wucin-gadi ba – Gwamnan Namadi

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.