Wani binciken ƙwaƙwaf da PREMIUM TIMES ta gudanar ya fallasw yadda ‘Yan Kwamitin Majalisa masu Binciken Harƙallar Daukar Ma’aikata ke karɓar rashawa da toshiyar-baki daga Shugabannin Ma’aikatun Gwamnati tsawon makonni da dama.
Binciken ya gano daga cikin shugabannin cibiyoyi da ma’aikatu da hukumomin da su ka riƙa tumbuza masu kuɗaɗe a wani asusun banki, har da shugabannin makarantun gaba da sakandare.
Kwamitin dai ya shafe kwanaki ya na gayyatar shugabannin cibiyoyi, hukumomi da ma’aikatun gwamnatin tarayya ana yi masu titsiye da fallasar yadda su ke ɗaukar ma’aikata ba bisa ƙa’idar da doka ta shimfiɗa ba.
Cikin hukumomin da aka titsiye har da Hukumar Jarabawar Shiga Jami’a Farfesa Ishaq Oloyede da Shugabar Hukumar Daidaiton Ɗaukar Ma’aikata ta Ƙasa, Khadija Ɗankaka.
‘Yan cuwa-cuwar mambobin Majalisar dai su 39 ne a cikin kwamitin, kuma an naɗa su tun a ranar 5 Ga Yuli.
An ɗauko mamba ɗaya daga cikin mambobin kowace jiha da kuma Abuja, sannan aka naɗa Yusuf Gadgi matsayin Shugaban Kwamiti. Gagdi na wakiltar Jihar Filato ne, kuma ɗan APC ne.
Sai dai kuma Oluwole Oke wanda ya bada shawarar a kafa kwamitin, kwata-kwata ko sunan sa babu a cikin mambobin kwamitin binciken.
Yayin da ɗimbin ‘yan Najeriya ke ta murnar kafa kwamitin, ganin yadda aka riƙa danne wa dubban ‘yan Najeriya damar samun aiki, ashe ba a sani ba kwamitin binciken ba kankare ba ne, tubalin toka ne.
Ashe duk barazanar da zare idanun da mambobin kwamitin ke yi a zauren bincike, duk talakawa ake raina wa wayau, ana kuma bagaras da su.
Yayin da ake yi wa shugabannin hukumomi, cibiyoyi da ma’aikatun gwamnati mazurai duniya na kallo a talbijin, da sun kulle ƙofa a tsakanin su kuma sai a kama cinikin yadda za a bai wa ‘yan kwamitin toshiyar baki, tsakanin ‘yan kwamiti da shugabannin na cibiyoyi, ma’aikatu da hukumomi.
Misali, a ranar 15 Ga Agusta, wasu mambobin kwamitin sun gana da Shugabannin Jami’o’in Gwamnatin Tarayya 51, aka umarci kowanen su ya biya Naira miliyan 3 don kada a tozarta shi a zauren bincike.
Farfesoshin dai sun yi ƙememe su ka ce ba za su biya ba, domin wasun ma makarantun ma su da cibiyoyi ko kuɗaɗe gwamnatin ba ta ba su wadatattu.
Daga nan aka rage farashi zuwa Naira miliyan biyu kowanen su zai bayar.
Daga nan aka bai wa kowane Farfesa akawun lamba 5400495458 ta Bankin Providus Bank, aka ce kowa ya zuba miliyan biyu a ciki.
Saboda tsabar rashin kunya har mambobin kwamitin su ka ce kowane shugaban jami’a ya rubuta sunan makarantar sa a wurin tura kuɗaɗen.”
Bayan nan kuma kwamitin ya yi ganawa da shugabannin manyan Kwalejojin Fasaha na gwamnatin tarayya 35, sai kuma wata ganawar da shugabannin Kwalejojin Ilmi mai Zurfi su 27, aka nemi kowanen sa ya biya miliyan 3, don kada a kunyata shi a gaban kyamara da ɗimbin ‘yan jarida masu haskaka ana kallo.
PREMIUM TIMES ta gano manyan makarantu sun biya jimillar naira miliyan 267, kuma Mambobin sun kwashe kuɗaɗen.
Hakan na nufin a lokacin da za su gama binciken cibiyoyi, ma’aikatu da hukumomi 1,500, kuɗaɗen da mambonin kwamitin binciken za su samu, za su iya tara biliyoyin nairori.
PREMIUM TIMES ta gano cewa asusun da aka riƙa tura kuɗaɗen mallakar Ama Business Solutions ne.
Kamfanin an kafa shi ranar 12 Ga Agusta, 2020, ya na da lasisin rajista mai lamba 3156889.
Adireshin sa shi ne Lamba 2249, Zone 4 Plaza, Titin Constantine, Wuse 4, Abuja.
Kamfanin na wasu mutum biyu ne, Abubakar Lawal Sambo da Abdulrahman Lawal Sambo.
Su biyun sun nuna cewa ‘yan kasuwa ne, amma Abdulrahman ya taɓa zama Hadimin tsohon Kakakin Majalisar Tarayya, Femi Gbajabiamila.
Discussion about this post