• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    RANAR ‘YANCI: ‘Yan Najeriya mazauna Landan sun nemi a yi wa gwamnatin NNPP a Kano adalci

    RANAR ‘YANCI: ‘Yan Najeriya mazauna Landan sun nemi a yi wa gwamnatin NNPP a Kano adalci

    JAllI-JOGAR BELIN DIEZANI A KOTUN LANDAN: Kotu ta hana Diezani fita yawon dare, da rana ma an ce ta maƙala na’urar gane duk lungun da ta shiga

    JAllI-JOGAR BELIN DIEZANI A KOTUN LANDAN: Kotu ta hana Diezani fita yawon dare, da rana ma an ce ta maƙala na’urar gane duk lungun da ta shiga

    Ƴan sanda sun damke wasu abokai ƴan kungiyar matsafa dake tsafi da kawunan mutane a Ilori

    Yadda ƴan sanda suka kama Ibrahim da ya yi garkuwa da Fatima, ya ƙarɓi kuɗi kuma ya yashe ta a Zariya

    Kotu ta kori gwamna Sule na Nasarawa, ta ce PDP ce ta yi nasara a zaɓen gwamna

    Kotu ta kori gwamna Sule na Nasarawa, ta ce PDP ce ta yi nasara a zaɓen gwamna

    Ku fito ku ceci mutanen jihar Kaduna kamar yadda kuka yi a zaben majalisun Tarayya da na sanatoci – Isah Ashiru

    An yi mana kwange a hukuncin kotu, za mu daukaka kara – Ashiru

    SSS

    TAKE HAƘƘIN ƊAN ADAM: Yadda SSS suka riƙa faffalla min mari, suka ja ni ƙasa girrrr, don kawai na ce su bi doka – Lauya Ogbankwa

    Muna ƙarancin malamai, a janye dokar hana ɗaukar sabbin malamai da gwamnatin tarayya ta ƙaƙaba – Jami’ar ABU

    Muna ƙarancin malamai, a janye dokar hana ɗaukar sabbin malamai da gwamnatin tarayya ta ƙaƙaba – Jami’ar ABU

    TONON ASIRI: An kama wani Dagaci cikin gungun mahara a lokacin batakashi da ‘Yan sanda

    ‘Yan bindiga sun kashe mutum shida a Kaduna

    Almajirai

    UNICEF ta saka Almajirai sama da 20,000 cikin rajistar tsarin agaza wa marasa karfi a Katsina

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    Hukumar CAF za ta binciki yadda mahaifiyar ɗan wasa ta mutu cikin 1986, shi kuma ya ce atabau cikin 1990 ta haife shi

    A karo na Uku, Moroko za ta ɗauki baƙuncin gasar cin kofin kwallon ƙafa na nahiyar Afrika a Janairun 2025

    NFF ta sake nada Chris Danjuma a matsayin kocin Falconets

    NFF ta sake nada Chris Danjuma a matsayin kocin Falconets

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    JERIN SUNAYE: Jami’o’i 51 da ba za su dauki dalibin da ya ci kasa da maki 180 a jarabawar JAMB ba

    TSARIN BAI WA ƊALIBAI RAMCE: Abubuwan da suka wajaba ɗalibai da iyaye su sani

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    RANAR ‘YANCI: ‘Yan Najeriya mazauna Landan sun nemi a yi wa gwamnatin NNPP a Kano adalci

    RANAR ‘YANCI: ‘Yan Najeriya mazauna Landan sun nemi a yi wa gwamnatin NNPP a Kano adalci

    JAllI-JOGAR BELIN DIEZANI A KOTUN LANDAN: Kotu ta hana Diezani fita yawon dare, da rana ma an ce ta maƙala na’urar gane duk lungun da ta shiga

    JAllI-JOGAR BELIN DIEZANI A KOTUN LANDAN: Kotu ta hana Diezani fita yawon dare, da rana ma an ce ta maƙala na’urar gane duk lungun da ta shiga

    Ƴan sanda sun damke wasu abokai ƴan kungiyar matsafa dake tsafi da kawunan mutane a Ilori

    Yadda ƴan sanda suka kama Ibrahim da ya yi garkuwa da Fatima, ya ƙarɓi kuɗi kuma ya yashe ta a Zariya

    Kotu ta kori gwamna Sule na Nasarawa, ta ce PDP ce ta yi nasara a zaɓen gwamna

    Kotu ta kori gwamna Sule na Nasarawa, ta ce PDP ce ta yi nasara a zaɓen gwamna

    Ku fito ku ceci mutanen jihar Kaduna kamar yadda kuka yi a zaben majalisun Tarayya da na sanatoci – Isah Ashiru

    An yi mana kwange a hukuncin kotu, za mu daukaka kara – Ashiru

    SSS

    TAKE HAƘƘIN ƊAN ADAM: Yadda SSS suka riƙa faffalla min mari, suka ja ni ƙasa girrrr, don kawai na ce su bi doka – Lauya Ogbankwa

    Muna ƙarancin malamai, a janye dokar hana ɗaukar sabbin malamai da gwamnatin tarayya ta ƙaƙaba – Jami’ar ABU

    Muna ƙarancin malamai, a janye dokar hana ɗaukar sabbin malamai da gwamnatin tarayya ta ƙaƙaba – Jami’ar ABU

    TONON ASIRI: An kama wani Dagaci cikin gungun mahara a lokacin batakashi da ‘Yan sanda

    ‘Yan bindiga sun kashe mutum shida a Kaduna

    Almajirai

    UNICEF ta saka Almajirai sama da 20,000 cikin rajistar tsarin agaza wa marasa karfi a Katsina

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    Hukumar CAF za ta binciki yadda mahaifiyar ɗan wasa ta mutu cikin 1986, shi kuma ya ce atabau cikin 1990 ta haife shi

    A karo na Uku, Moroko za ta ɗauki baƙuncin gasar cin kofin kwallon ƙafa na nahiyar Afrika a Janairun 2025

    NFF ta sake nada Chris Danjuma a matsayin kocin Falconets

    NFF ta sake nada Chris Danjuma a matsayin kocin Falconets

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    JERIN SUNAYE: Jami’o’i 51 da ba za su dauki dalibin da ya ci kasa da maki 180 a jarabawar JAMB ba

    TSARIN BAI WA ƊALIBAI RAMCE: Abubuwan da suka wajaba ɗalibai da iyaye su sani

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

Sako Zuwa Ga Al’ummar Jihar Zamfara Baki Daya, Daga Imam Murtadha Gusau

Premium Times HausabyPremium Times Hausa
August 19, 2023
in Ra'ayi
0
Sako Zuwa Ga Al’ummar  Jihar Zamfara Baki Daya, Daga Imam Murtadha Gusau

Da Sunan Allah, Mai Rahama, Mai Jinkai

Assalamu alaikum wa rahmatullah wa bara ka tuh

Ya ‘yan uwana Zamfarawa masu albarka, ya kamata mu sani, da shi Dauda Lawal da ya zama Gwamnan jihar Zamfara da shi Bello Muhammad Matawalle da ya zama Ministan Najeriya duk wannan daga Allah ne, cikin su ba wanda ya ba kansa wannan matsayi. Babu wanda wayonsa ne ko dabararsa ya bashi. Munyi imani da Allah, a matsayin mu na Musulmi cewa, Allah shine yake bayar da mulki da matsayi ga wanda yaso. Don haka, ya zama tilas, wajibi kuma dole muyi masu addu’a dukkaninsu, muyi masu fatan alkhairi, Allah ya basu sa’a, Allah yasa suci nasara, Allah yasa ace gwamma da aka yi. Allah yasa su zamar wa jihar Zamfara alkhairi da Najeriya baki daya, kuma Allah ya fitar da su kunyar duniya da ta lahira, amin.

Amma mutum ya koma gefe yana soke-soke da zage-zage da cin mutunci; ko ya kasance yana rubuce-rubucen banza a social media, ko ya shiga rediyo ko talabijin yana babatun banza, don yana goyon bayan Gwamna ko yana goyon bayan Minista, to wallahi duk wannan bai yi ba, kuma bai dace ba, kuma a matsayin mu na Musulmi, mu sani, wannan haramun ne, haramun ne, haramun ne!

Duk mai kishin jihar Zamfara da Najeriya da gaske, duk mai son a samar da tsaro da ci gaba da kwanciyar hankali, to kamata yayi ya dage da addu’a da rokon Allah Subhanahu wa Ta’ala yasa wadannan shugabanni su zama alkhairi a gare mu baki daya.

Don haka ina kira da muji tsoron Allah, muyi masu addu’a, muyi wa jihar mu da kasar mu addu’a.

Duk siyasar da muke yi, mu tuna cewa mu Musulmi ne, mu al’ummah ce musulma. Don haka shi Musulmi yana da dokoki da ka’idodin da suke yi masa jagoranci a cikin dukkanin rayuwarsa, ba haka kawai yake rayuwa sagaga ba! A tare da shi akwai mala’iku masu rubuta duk abunda yayi, na sharri ko na alkhairi.

Sannan su kuma wadannan shugabanni guda biyu, wato da shi Gwamna Dauda Lawal da kuma shi Minista Muhammad Bello Matawalle, ina rokon su, ina kiran su, da suji tsoron Allah Subhanahu wa Ta’ala. Su sani cewa, su jarabawa ne da Allah ya jarrabi Zamfarawa da su. Don haka, ya zama wajibi su hada kai domin su kawo wa jihar Zamfara da Najeriya baki daya alkhairi da ci gaban da zai amfani kowa da kowa. Kar su yarda su zama sharri ga al’ummarsu. Suyi kokari su zama alkhairi a garesu. Kar su yarda da masu zuga, kar su yarda da ‘yan-bani-na-iya, ‘yan kanzagi, masu banbadanci, wadanda su a koda yaushe, fadan shugabanni da rigimarsu da hayaniyarsu shine hanyar cin abincinsu. Irin wadannan mutane, wallahi babu wani alkhairi a tare da su sai sharri.

Gwamna Dauda Lawal, Minista Muhammad Bello Matawalle, ku sani, ku biyu din nan, Allah zai tashe ku a gabansa, a filin alkiyama, domin yi maku hisabi akan wannan jagoranci da ya dora maku. A wannan rana wallahi babu wani magoyi bayan ku da zai iya fitar da ku illa ayukkanku da kuka gabatar. Don haka, kar ku taba yarda da zugar wani magoyi baya, wanda sam a ranar lahira ta kan sa yake yi, kuma kuna ta kan ku. Don haka don Allah ku kiyaye.

Wallahi kaunar da nike yi maku tsakanina da Allah, da kuma kishi na ga jiha ta da kasa ta, shi yasa na rubuta wannan sako mai albarka. Domin ina kallon duk abunda yake faruwa kuma yake gudana a jiharmu. Idan lamarin yaci gaba a haka to tabbas, jiharmu da al’ummarmu dama ku kan ku, ba za kuji dadi ba.

Ku manta da maganar banbancin jam’iyyar da ke tsakaninku, ku manta da banbancin siyasar da ke tsakaninku, kuji tsoron mahaliccinku, ku kalli al’ummarku, kuyi kokari ku hada kai domin tunkarar rashin tsaro da yunwa da talaucin da suke addabar jiharmu ta Zamfara mai albarka.

Muhammad Bello Matawalle, a matsayin da Allah ya baka na Ministan tsaro, ya zama tilas, in dai kana son tsira a gaban Allah, ka hada kai da Gwamna Dauda Lawal, kuyi aiki tare, domin samar da kyakkyawar natija.

Gwamna Dauda Lawal, a matsayin ka na Gwamnan jihar Zamfara, wanda Allah ya damka amanar tsaron jihar Zamfara da ci gabanta, da zaman lafiyarta a hannunka, kai ma ya zama tilas, in dai kana son tsira a gaban Allah, ka hada kai da Minista Muhammad Bello Matawalle, kuyi aiki tare, ba tare hangen wani banbaci na jam’iyya ko na siyasa ba, domin kawo wa jihar Zamfara da ma Najeriya baki daya ci gaba.

Wannan shine gaskiyar magana, wadda duk wani masoyinku na gaskiya, wannan ya kamata ya gaya maku. Duk wanda zai gaya maku akasin haka, duk wanda zai zuga ku domin ku zama makiyan juna, to ku sani, ina mai yi maku rantsuwa da Allah, wanda babu abun bautawa da gaskiya sai shi, wannan mutum ko waye shi, to ba masoyinku bane. Makiyin kune, wanda yake so ya jefa ku cikin rame, ya bar ku da jangwam a gaban Allah Subhanahu wa Ta’ala.

Sannan dukkanin manyan ‘yan siyasarmu na jihar Zamfara suma ya zama dole su mayar da hankali wurin zamar wa jihar Zamfara da Najeriya baki daya alkhairi: irin su mai girma tsohon Gwamnan jihar Zamfara Alhaji Ahmad Sani Yariman Bakura, mai girma tsohon Gwamna Sanata Abdul-Aziz Yari, mai girma tsohon Sanata Marafa, mai girma Dan Majalisa Aminu Sani Jaji, mai girma Sanata Ikra Aliyu Bilbis, mai girma Sanata Sahabi Ya’u Kaura, mai girma Dan Majalisa Kabiru Amadu Mai Palace, kI da duk ma wadanda ban ambata ba, dukkanin masu ruwa da tsaki a harkar siyasar jihar Zamfara, ya zama wajibi a gare mu da muji tsoron Allah, mu zama alkhairi ga jihar mu mai albarka.

Gaskiyar magana ita ce, dukkaninku kuna da magoya baya, kuna da masoya, akwai dimbin jama’ar da suke bayanku, don haka wuka da nama duk a hannunku suke. Idan kun gyara kun sani, kuma idan kun bata kun sani.

Sannan duk wanda yayi da kyau, ya sani, Allah zai yaba, kuma al’ummah zasu yaba. Duk kuma wanda ya bata, to ya sani, zai jawo wa kansa fushin Allah, kuma al’ummah zasu yi Allah waddai da shi.

Allah yasa mu dace, ya ganar da mu, amin.

Daga dan uwanku: Imam Murtadha Muhammad Gusau. Juma’ah, 18/08/2023. 08038289761.

Tags: AbujaHausaImamMurtadhaNews
Previous Post

AIKIN TSAUTSAYI KO AIKIN SHAIƊAN: An tsinci gawar wata mai wa’azi a ɗakin otal ɗin da wani Babban Limamin Coci ya kai ta cikin dare

Next Post

Atiku ya yaba wa Farfesa Gwarzo kan samun lasisin kafa sabbin jami’o’i biyu da ya samu daga NUC

Premium Times Hausa

Premium Times Hausa

Next Post
Atiku ya yaba wa Farfesa Gwarzo kan samun lasisin kafa sabbin jami’o’i biyu da ya samu daga NUC

Atiku ya yaba wa Farfesa Gwarzo kan samun lasisin kafa sabbin jami’o’i biyu da ya samu daga NUC

Discussion about this post

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • Tinubu ya aika da sunan wanda ya musanya El-Rufai da shi da sunayen wasu mutum uku majalisa don zama ministoci
  • RANAR ‘YANCI: ‘Yan Najeriya mazauna Landan sun nemi a yi wa gwamnatin NNPP a Kano adalci
  • Fasinjoji 40 sun nitse cikin ruwa, bayan kifewar jirgin su a Kogin Yauri
  • DALLA-DALLA: Yadda aka cimma yarjejeniya tsakanin gwamnati da ƙungiyoyin ƙwadago
  • JAllI-JOGAR BELIN DIEZANI A KOTUN LANDAN: Kotu ta hana Diezani fita yawon dare, da rana ma an ce ta maƙala na’urar gane duk lungun da ta shiga

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.