• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Ku fito ku ceci mutanen jihar Kaduna kamar yadda kuka yi a zaben majalisun Tarayya da na sanatoci – Isah Ashiru

    An yi mana kwange a hukuncin kotu, za mu daukaka kara – Ashiru

    SSS

    TAKE HAƘƘIN ƊAN ADAM: Yadda SSS suka riƙa faffalla min mari, suka ja ni ƙasa girrrr, don kawai na ce su bi doka – Lauya Ogbankwa

    Muna ƙarancin malamai, a janye dokar hana ɗaukar sabbin malamai da gwamnatin tarayya ta ƙaƙaba – Jami’ar ABU

    Muna ƙarancin malamai, a janye dokar hana ɗaukar sabbin malamai da gwamnatin tarayya ta ƙaƙaba – Jami’ar ABU

    TONON ASIRI: An kama wani Dagaci cikin gungun mahara a lokacin batakashi da ‘Yan sanda

    ‘Yan bindiga sun kashe mutum shida a Kaduna

    Almajirai

    UNICEF ta saka Almajirai sama da 20,000 cikin rajistar tsarin agaza wa marasa karfi a Katsina

    Majalisar Tarayya ta ce a soke ƙarin kuɗin makaranta da aka yi wa ɗaliban jami’o’i da na Kwalejojin Gwamnatin Tarayya

    KALUBALEN DA KE GABAN MAJALISAR WAKILAI TA ƘASA: Gaganiya da matsalar raɗaɗin tsadar rayuwa, matsalar tsaro da sauran su da ake fuskanta a kasa

    Yadda sojojin sama sun ragargaza sansanonin ‘yan bindiga a jihohin Katsina, Zamfara, Sokoto da Kaduna

    RASHIN TSARO: Tinubu ya amince da sayo jiragen sama masu saukar ungulu 12 ga sojojin Najeriya – Lagbaja

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    Ƴan ta’adda sun gamu da fushin sojojin Najeriya, sojoji sun kashe 50 sun kama 60

    GRAINS MARKET AT KAFIN MADAKI DISTRICT IN GANJUWA

    Yari ya raba tallafin tirela 145 cike maƙil da buhunan masara 145 ga mabuƙata a Zamfara

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    Hukumar CAF za ta binciki yadda mahaifiyar ɗan wasa ta mutu cikin 1986, shi kuma ya ce atabau cikin 1990 ta haife shi

    A karo na Uku, Moroko za ta ɗauki baƙuncin gasar cin kofin kwallon ƙafa na nahiyar Afrika a Janairun 2025

    NFF ta sake nada Chris Danjuma a matsayin kocin Falconets

    NFF ta sake nada Chris Danjuma a matsayin kocin Falconets

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    JERIN SUNAYE: Jami’o’i 51 da ba za su dauki dalibin da ya ci kasa da maki 180 a jarabawar JAMB ba

    TSARIN BAI WA ƊALIBAI RAMCE: Abubuwan da suka wajaba ɗalibai da iyaye su sani

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Ku fito ku ceci mutanen jihar Kaduna kamar yadda kuka yi a zaben majalisun Tarayya da na sanatoci – Isah Ashiru

    An yi mana kwange a hukuncin kotu, za mu daukaka kara – Ashiru

    SSS

    TAKE HAƘƘIN ƊAN ADAM: Yadda SSS suka riƙa faffalla min mari, suka ja ni ƙasa girrrr, don kawai na ce su bi doka – Lauya Ogbankwa

    Muna ƙarancin malamai, a janye dokar hana ɗaukar sabbin malamai da gwamnatin tarayya ta ƙaƙaba – Jami’ar ABU

    Muna ƙarancin malamai, a janye dokar hana ɗaukar sabbin malamai da gwamnatin tarayya ta ƙaƙaba – Jami’ar ABU

    TONON ASIRI: An kama wani Dagaci cikin gungun mahara a lokacin batakashi da ‘Yan sanda

    ‘Yan bindiga sun kashe mutum shida a Kaduna

    Almajirai

    UNICEF ta saka Almajirai sama da 20,000 cikin rajistar tsarin agaza wa marasa karfi a Katsina

    Majalisar Tarayya ta ce a soke ƙarin kuɗin makaranta da aka yi wa ɗaliban jami’o’i da na Kwalejojin Gwamnatin Tarayya

    KALUBALEN DA KE GABAN MAJALISAR WAKILAI TA ƘASA: Gaganiya da matsalar raɗaɗin tsadar rayuwa, matsalar tsaro da sauran su da ake fuskanta a kasa

    Yadda sojojin sama sun ragargaza sansanonin ‘yan bindiga a jihohin Katsina, Zamfara, Sokoto da Kaduna

    RASHIN TSARO: Tinubu ya amince da sayo jiragen sama masu saukar ungulu 12 ga sojojin Najeriya – Lagbaja

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    Ƴan ta’adda sun gamu da fushin sojojin Najeriya, sojoji sun kashe 50 sun kama 60

    GRAINS MARKET AT KAFIN MADAKI DISTRICT IN GANJUWA

    Yari ya raba tallafin tirela 145 cike maƙil da buhunan masara 145 ga mabuƙata a Zamfara

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    Hukumar CAF za ta binciki yadda mahaifiyar ɗan wasa ta mutu cikin 1986, shi kuma ya ce atabau cikin 1990 ta haife shi

    A karo na Uku, Moroko za ta ɗauki baƙuncin gasar cin kofin kwallon ƙafa na nahiyar Afrika a Janairun 2025

    NFF ta sake nada Chris Danjuma a matsayin kocin Falconets

    NFF ta sake nada Chris Danjuma a matsayin kocin Falconets

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    JERIN SUNAYE: Jami’o’i 51 da ba za su dauki dalibin da ya ci kasa da maki 180 a jarabawar JAMB ba

    TSARIN BAI WA ƊALIBAI RAMCE: Abubuwan da suka wajaba ɗalibai da iyaye su sani

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

RA’AYIN PREMIUM TIMES: RIKICIN SHUGABANCIN NIJAR: Sulhu ne mafi alheri ba afka wa Nijar da yaƙi ba

Premium Times HausabyPremium Times Hausa
August 14, 2023
in Babban Labari
0
IN ZA KA FAƊI, FAƊI GASKIYA: Matsaloli 15 da za su dabaibaye Najeriya idan ta afka wa Nijar da yaƙi – OSPRE

Tun daga ranar da sojojin juyin mulki suka kifar da Gwamnatin Mohammed Bazoum a Nijar, a ranar 26 Ga Yuli, har yau mahukuntan ba su bi umarni ko guda ɗaya da ƙungiyar ECOWAS ta gindiya masu ba, duk kuwa da cewa an ƙaƙaba wa ƙasar takunkumi. Bazoum, shugaban da aka hamɓaras har yau ya na tsare shi da iyalan sa.

Fahimtar matsalar Nijar ta ƙara faɗaɗa ta yadda ake kallon yadda Amurka da Faransa su ke zaramboton shiga tsamo-tsamo wajen ‘yancin ƙasar Nijar.

A gefe ɗaya, su kuma mahukuntan sojojin mulki sun yi amfani da hankalin al’ummar ƙasar sama da miliyan 25 wajen nuna ƙiyayya Turawan mulkin mallaka, lamarin da hakan ya nuna sun shirya jan tsawon lokaci ana fafatawa da su, kafin kafin su sauka su maida mulki.

To a nan ne fa diflomasiyya za ta fuskanci ƙalubale, haka ita kan ta ECOWAS a ƙarƙashin shugaban Najeriya, Bola Tinubu da ma duniya baki ɗaya.

Jamhuriyar Nijar na ɗaya daga cikin ƙasashen da talauci ya fi yi wa katutu a duniya. Ta na sahun gaban ƙasashen da ake buga misalin irin ƙuncin rayuwar da ake fama da shi yanzu haka a duniya sanadiyyar matsalar koma-bayan tattalin arzikin da ya buwayi duniya a yanzu.

A gefe ɗaya kuma Turawan mulki na ƙasar Faransa sun tatse mafi yawan dukiyar ƙasar, to kuma har yau tun bayan samun ‘yanci, Nijar ba ta samu wani ci gaban a zo a gani ba daga hannun shugabannin da su ka riƙa mulkar ta tun 1960, in banda makwaɗaitan shugabanni masu yin birgima a kan dukiyar ƙasar, su na ƙara danna talakawan Nijar cikin ƙangin talauci.

Ana ta ruruta batun arzikin albarkatun yunaniyan a Nijar. To amma a gaskiyar magana yuraniyan ɗin Nijar fa bai wuce kashi 6 bisa 100 na yawan yuraniyan ɗin da ke duniya ba. Saboda ko a Faransa ma da ake kukan cewa ta na tatse yuraniyan ɗin Nijar, to mafi yawan wanda ta ke amfani da shi ba na Nijar ba ne, daga Kazakhstan ta ke shigo da shi.

Gaskiyar lamari Nijar ta na cikin wani yanayi, domin ba ta iya noma abincin da ƙasar ke buƙata. Kashi 1 bisa 5 na abincin da ake buƙata a Nijar duk daga waje ake shiga da shi. Dalili kenan ma ƙasar ta dogara a kan tallafin dala biliyan 2 da ta ke samu a kowace shekara.

Ya kamata sojojin mulkin Nijar su yi karatun ta-natsu, su fahimci cewa zara idanu da fankamar su fa ba za ta kai Nijar ko’ina ba, ballantana su iya fitar da ƙasar daga matsalar tattalin arzikin da ya jefa al’ummar ta cikin raɗaɗin tsadar rayuwa. Idan ba a ɗauki matakin da ya dace ba, lamarin zai iya jefa ƙasar cikin ruɗani.

Hana jiragen ruwa shiga yankin Ukaraniya da Rasha ya yi, ya haddasa tsakon samun tallafin abincin da Majalisar Ɗinkin Duniya ke saye daga Ukaraniya ya na bai wa Afrika, wanda zuwa shekara mai zuwa aka tsara yawan wanda Afrika ke samu zai ƙarasa kaiwa Yuro miliyan 500. Saboda haka Nijar na buƙatar wannan tallafi, haka ta na buƙatar tallafin Dala miliyan 153 na litattafai daga Amurka a wannan shekara. Idan ba haka ba kuwa, to ƙasar za ta ƙara shiga ruɗanin ƙuncin rayuwa, wanda talakawa kaɗai zai shafa.

Ya kamata sojojin mulkin Nijar su yi la’akari da wannan mawuyacin hali da ƙasar ke ciki, da kuma wanda za su ƙara jefa ƙasar a yanzu.

PREMIUM TIMES na kira ga ECOWAS da Shugabannin Ƙasashen ECOWAS cewa su ci gaba da zurfafa bin turbar diflomasiyya domin sulhunta rikicin shugabancin Nijar. Kada takunkumin da aka ƙaƙaba wa ƙasar a yanzu ya toshe hanyar iya farfaɗo da ƙasar bayan mulkin Tchiani.

Misali, yanke wutar lantarki da aka yi a Nijar zai ƙara gurgunta tattalin arzikin ƙasar, wanda dama shure-shuren mutuwa tattalin arzikin ke yi.

Kada a tsaya ana kafa hujja da gutsiri-tsomar zargin salwantar dala miliyan 153 na sayen makamai a matsayin hujjar halasta juyin mulki a Nijar.

Tabbas cin hanci da rashawa abu ne da ya haifar da kasa ci gaban Nijar tun bayan samun ‘yanci. To kuma ba juyin mulkin su Tchiani ke farko ba, wajen kafa hujja da cin hanci da rashawa a matsayin dalilin kifar da gwamnatin dimokraɗiyya.

Amma kuma wannan zargin salwantar kuɗaɗen makamai har dala miliyan 153, tilas a binciki yadda aka yi da kuɗaɗen.

Kada a manta, tun shekaru uku da su ka wuce PREMIUM TIMES ta bada labarin wannan harƙallar salwantar dala miliyan 153 ta sayen makamai.

Don haka zai yi kyau a ga yadda za ta ƙarke tsakanin tsohon Shugaban Ƙasa Mahammoudou Issoufou da kuma Tchiani, wanda a baya ya yi aiki ƙarƙashin gwamnatin Issoufou, gwamnatin da kuɗaɗen su ka salwanta a ƙarƙashin ta.

A na ta ɓangaren, bai yiwuwa Faransa ta riƙa amfani da wata yarjejeniyar gare da ya tsara fiye da shekaru 60, ya na amfani da ita, ta na yin kane-kane cikin sha’anin ƙarar da ta karɓi ‘yancin kai tun tun 1960.

Dama kuma yarjejeniya ce da ƙarara ke nuna cewa Faransa ɗin ce ke tatsar ƙasar da duk ta raina.

Faransa, ƙasar da ta tara shugabannin duniya a cikin watan Yuni domin shata sabuwar alƙiblar cin moriyar juna, bai kamata kuma a ce ita ke yin riƙo da wata tsohuwar yarjejeniyar da ta naniƙe wa ƙasashen da ta mulka ba. Ta ƙyale su hakanan su samar wa kan su mafita.

Babban kuskure ne ‘yan Nijar da irin su Mali da Burkina Faso su riƙa kallon cewa mutanen da ke sanye da khaki ne za su ceto su daga matsalolin su.

Shi kan sa Tchiani na Nijar ai tun cikin 2011 ya ke Shugaban Zaratan Sojojin Tsaron Fadar Shugaban Ƙasa. Ashe kenan duk wata matsala da sojoji su ka haifar, ya na daga ciki kenan.

Don haka batun cewa ya ƙwace mulki ne don ya ceto ƙasar, abin shakku ne. PREMIUM TIMES na yin kira gare shi ya katse gugumarar neman goyon bayan da ya ke yi a Yamai, ya bayyana lokacin maida mulki ga zaɓaɓɓiyar gwamnatin dimokraɗiyya.

Kuma wannan matsaya ce ECOWAS da Najeriya da Najeriya su ka ɗauka. Najeriya na fuskantar ƙalubale, domin abin da ya shafi Nijar ya shafe ta, kasancewa al’ummar Hausawa da Fulani na Arewacin Najeriya kisan ‘yan’uwan juna su ke da na Nijar.

A ɗaya gefen kuma abin da ke faruwa a yanzu da waɗanda su ka faru a baya, sun nuna kakaf a ECOWAS babu wata ƙasa da ke da ƙarfin sojan da ke iya daƙile matsalar tsaro a cikin ta.

Saboda haka su ma Sojojin Najeriya ba su da wani shiri na tattago wani yaƙi har cikin wata ƙasa a yanzu.

A yanzu an watsa sojojin Najeriya su na aikin tsaro a jihohi 34 cikin 36 na ƙasar nan. Ga shi ƙarara Boko Haram ‘yan ISWAP sun sake dannowa, ga dandazon ‘yan gudun hijira a kan iyakoki, ga kuma dandazon ‘yan bindiga. To da me za a ji?

Ƙarara dai ‘yan Najeriya sun nuna cewa ba su son a karkashe ‘yan’uwan su ‘yan Nijar haka kawai ba gaira ba dalili.

Saboda haka, PREMIUM TIMES na kira ga dukkan masu ruwa da tsaki a cikin Najeriya da ƙasashen duniya su ci gaba da matsin-lambar yin sulhu a cikin ruwan sanyi. Amma afka wa Nijar da yaƙi ba alheri ba ne.

Tags: AbujaEcowasHausaNewsNijarPREMIUM TIMESTinubu
Previous Post

RAƊAƊIN RAYUWA: Jami’ar Bayero ta samar wa ma’aikatan ta tallafin kekuna da manyan motocin hawa da tallafin abinci

Next Post

Ƴan bindiga sun sun yi garkuwa da ɗan sarkin Bungudu, sabuwar amarya da wasu mutum 5 a Zamfara

Premium Times Hausa

Premium Times Hausa

Next Post
Ƴan bindiga sun sun yi garkuwa da ɗan sarkin Bungudu, sabuwar amarya da wasu mutum 5 a Zamfara

Ƴan bindiga sun sun yi garkuwa da ɗan sarkin Bungudu, sabuwar amarya da wasu mutum 5 a Zamfara

Discussion about this post

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • Ba za mu bari a yi mana rinto da rana tsaka ba, mutanen Kaduna mu suka zaɓa – Ashiru
  • TATTALIN ARZIKI: Gwamnatin Tarayya ta tara naira tiriliyan 10.18 a 2022
  • KURUNKUS: Kwamitin Amintattun jam’iyyar NNPP sun kori Kwankwaso daga Jam’iyyar Kwatakwata
  • Kotu ta ci tarar gwamnatin Kano Naira biliyan 30 saboda rusa ginegine ba bisa ka’ida ba
  • Yadda gaggan ‘Yan bindiga da suka addabi Arewa su ka yi taron sulhu da tawagar gwamnatin Tarayya a Katsina

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.