Babban Sakataren Ma’aikatar Harkokin Wajen Najeriya, Adamu Lamuwa, ya tabbatar da cewa Najeriya ba za ta yi amfani da ƙarfin soja kan sojojin mulkin Nijar ba, har sai ta kasance babu wata makawa sai an yi yaƙin sannan za su sauka su bayar da mulkin.
“Amfani da ƙarfin soja a rikicin Nijar shi ne mataki na ƙarshe, bayan an bi dukkan wasu matakan sasanci sun faskara. Kuma ina fatan lamarin ba zai kai ga gwabza yaƙin ba.” Cewar Lamuwa.
Ya bayyana haka a ranar Juma’a, yayin da ya ke wa jami’an diflomasiyyar ƙasashe masu ofishin jakadanci jawabi a Abuja.
Biyo bayan tsamin da dangantaka ta yi tsakanin ECOWAS da Nijar, ƙungiyar ta gayyaci Hafsan Hafsoshin Tsaron ƙasashen su yi taron gaggawa.
Sun fara taro a ranar Laraba, wanda ake sa ran kammalawa a yau Juma’a.
Najeriya ce a matsayin ta na babbar ƙasar da ta fi ƙarfin tattalin arziki a Afrika da ECOWAS, har ma da yawan sojoji, za ta fi bayar da gudunmawar zaratan sojojin da za su yi artabu a Nijar.
Sai dai kuma da aka tambayi Lamuwa ko da gaske ne Nijar ta kori Jakadan Najeriya da ke ƙasar, sai ya ce shi dai har yanzu ba a sanar da shi da baki ko a rubuce ba.
A Najeriya, Shugaba Bola Tinubu wanda shi ne Shugaban ECOWAS, ya rubuta wa Majalisar Dattawa sanarwar shirin afka wa Nijar da yaƙi, don ƙwatar wa Bazoum mulki daga hannun sojoji.
Yayin da Najeriya ke tsakiyar fama da ‘yan bindiga a Arewa maso Yamma da Arewa ta Tsakiya, sai kuma Boko Haram, Shugaba Bola Tinubu ya rubuta wa Majalisar Dattawa wasiƙar sanar da su matakan da ECOWAS ta ɗauka domin tabbatar da an dawo da mulkin farar hula a Jamhuriyar Nijar.
Cikin wasiƙar wadda ke ɗauke da sanarwar takunkumin da ECOWAS ta ƙaƙaba wa Nijar, waɗanda har wasu sun fara aiki, har da shirye-shiryen ɗaukar matakin yin amfani da ƙarfin soja, domin a ƙwatar wa hamɓararren shugaban ƙasar, Mohammed Bazoum mulkin sa daga hannun sojoji.
Akwai matakan datse wutar lantarki a Nijar daga wutar lantarki, sai kuma dakatar da shigar da kaya daga Najeriya da ƙasashen ECOWAS zuwa cikin Nijar.
Sai dai kuma labarin baya-bayan nan ya tabbatar da cewa Nijar ta yanke hulɗa da Najeriya, bayan tattaunawa tsakanin sojojin mulkin ƙasar da tawagar shiga tsakanin ECOWAS da Nijar a ƙarƙashin tsohon Shugaban Najeriya, Janar Abdulsalami Abubakar ta tashi baram-baram.
PREMIUM TIMES ta ruwaito Bazoum ya ce tsige shi zai haifar wa Nijar, ECOWAS, Afrika da duniya gagarimar matsala.
Shugaban ƙasar Nijar da sojoji suka hamɓare, a karon farko ya yi magana daga inda ya ke a tsare.
Bazoum ya yi magana ranar Juma’a, kwanaki tara bayan hamɓarar da Gwamnatin sa.
Da ya ke magana a inda ya ke tsare, Bazoum ya ce hamɓarar da Gwamnatin sa gangaci ne, kuma babu wani dalili ko hujjar da sojoji za su kifar da gwamnatin sa, wadda al’ummar Nijar su ka zaɓe su.
“Juyin mulkin da sojoji suka yi min a ranar 26 Ga Yuli, ba shi da wani dalili ko hujja.
“Domin juyin mulkin zai haifar da mummunan sakamako a yankin mu da ma duniya baki ɗaya.”
Haka Bazoum ya faɗa a shafin sa na X Tiwita.
Babu wata sanarwa mai tabbatar da cewa bayanan sa ne, amma ganin yadda AU, Bankin Duniya da Bill Gates ke bibiyar shafin na sa, hakan ya ƙara tabbatar da cewa Bazoum ɗin ne ya yi rubutaccen bayanin.
Bazoum ya roƙi a ƙasashen ECOWAS da duniya kada a bari sojoji su gurgunta dimokraɗiyya.
Yayin da Bazoum ya roƙi Amurka da sauran masu faɗa a ji, su taimaka masa mulki ya koma hannun sa.
A cikin jawabin na sa, ya bayyana irin gagarimar nasarorin da gwamnatin sa ta samar wajen tsaron Nijar yankin ECOWAS.
Haka kuma Bszoum ya yi Allah wadai ƙasashen Mali da Burkina Faso, waɗanda suka nuna goyon bayan su ga gwamnatin sojojin Nijar.
Discussion about this post