• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Yadda sojojin sama sun ragargaza sansanonin ‘yan bindiga a jihohin Katsina, Zamfara, Sokoto da Kaduna

    RASHIN TSARO: Tinubu ya amince da sayo jiragen sama masu saukar ungulu 12 ga sojojin Najeriya – Lagbaja

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    Ƴan ta’adda sun gamu da fushin sojojin Najeriya, sojoji sun kashe 50 sun kama 60

    GRAINS MARKET AT KAFIN MADAKI DISTRICT IN GANJUWA

    Yari ya raba tallafin tirela 145 cike maƙil da buhunan masara 145 ga mabuƙata a Zamfara

    Masu maular ‘kudaden kama haya’ a hannun Ayu ke hana sasanta rikicin PDP -Wike

    Ministan Abuja ya bada wa’adin gina filaye 189 cikin wata uku, ko ya ƙwace su

    DA ƊUMI-ƊUMI: Gobara ta tashi a Kotun Ƙoli, ta babbake ofishin manyan alƙalai uku

    DA ƊUMI-ƊUMI: Gobara ta tashi a Kotun Ƙoli, ta babbake ofishin manyan alƙalai uku

    TSUMAGIYAR KAN HANYA: An umarci ‘yan sandan Abuja su riƙa binciken motar ko wa kuma ko ɗan wa

    Kotu ta daure magidancin da ya guntile hannun abokinsa kan zargin lalata da matarsa

    Jami’an Kwastam sun kama haramtattun kaya na miliyoyin naira a Katsina

    Hukumar Kwastam ta kama haramtattun kaya na naira biliyan 6.6 a jihar Ogun

    American University of Nigeria Student -Crt- Google

    Malaman jami’o’i na roƙon a biya su albashin wata da watannin da aka riƙe masu

    ‘Yan sanda sun damke faston da ake zargin yayi wa ‘yar shekara 19 fyade

    Kotu ta yanke wa mahaifin da ya yi shekara 9 yana lalata da ƴa’ƴan sa mata biyu

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    JERIN SUNAYE: Jami’o’i 51 da ba za su dauki dalibin da ya ci kasa da maki 180 a jarabawar JAMB ba

    TSARIN BAI WA ƊALIBAI RAMCE: Abubuwan da suka wajaba ɗalibai da iyaye su sani

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Yadda sojojin sama sun ragargaza sansanonin ‘yan bindiga a jihohin Katsina, Zamfara, Sokoto da Kaduna

    RASHIN TSARO: Tinubu ya amince da sayo jiragen sama masu saukar ungulu 12 ga sojojin Najeriya – Lagbaja

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    Ƴan ta’adda sun gamu da fushin sojojin Najeriya, sojoji sun kashe 50 sun kama 60

    GRAINS MARKET AT KAFIN MADAKI DISTRICT IN GANJUWA

    Yari ya raba tallafin tirela 145 cike maƙil da buhunan masara 145 ga mabuƙata a Zamfara

    Masu maular ‘kudaden kama haya’ a hannun Ayu ke hana sasanta rikicin PDP -Wike

    Ministan Abuja ya bada wa’adin gina filaye 189 cikin wata uku, ko ya ƙwace su

    DA ƊUMI-ƊUMI: Gobara ta tashi a Kotun Ƙoli, ta babbake ofishin manyan alƙalai uku

    DA ƊUMI-ƊUMI: Gobara ta tashi a Kotun Ƙoli, ta babbake ofishin manyan alƙalai uku

    TSUMAGIYAR KAN HANYA: An umarci ‘yan sandan Abuja su riƙa binciken motar ko wa kuma ko ɗan wa

    Kotu ta daure magidancin da ya guntile hannun abokinsa kan zargin lalata da matarsa

    Jami’an Kwastam sun kama haramtattun kaya na miliyoyin naira a Katsina

    Hukumar Kwastam ta kama haramtattun kaya na naira biliyan 6.6 a jihar Ogun

    American University of Nigeria Student -Crt- Google

    Malaman jami’o’i na roƙon a biya su albashin wata da watannin da aka riƙe masu

    ‘Yan sanda sun damke faston da ake zargin yayi wa ‘yar shekara 19 fyade

    Kotu ta yanke wa mahaifin da ya yi shekara 9 yana lalata da ƴa’ƴan sa mata biyu

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    JERIN SUNAYE: Jami’o’i 51 da ba za su dauki dalibin da ya ci kasa da maki 180 a jarabawar JAMB ba

    TSARIN BAI WA ƊALIBAI RAMCE: Abubuwan da suka wajaba ɗalibai da iyaye su sani

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

GOBARA DAGA TEKU: Majalisar Legas ta yi fatali da sunayen kwamishinoni 17, bayan Musulman Legas sun yi ƙorafin danniya da wariya

Ashafa MurnaibyAshafa Murnai
August 24, 2023
in Labarai
0
GOBARA DAGA TEKU: Majalisar Legas ta yi fatali da sunayen kwamishinoni 17, bayan Musulman Legas sun yi ƙorafin danniya da wariya

Majalisar Dokokin Jihar Legas ta yi fatali da sunayen kwamishinoni 17 daga cikin 39 ɗin da Gwamna Babajide Sanwo-Olu ya aika mata domin tantancewa.

Daga cikin waɗanda ta yi fatali da su ɗin, akwai guda shida waɗanda kwamishinonin Sanwo-Olu ne a zangon farko, yanzu kuma ya ke so su maimaita.

Kakakin Yaɗa Labaran Majalisar Dokokin Jihar Legas, Bisola Branco-Adekoya ce ta fitar da wannan sanarwa, kuma ta aiko wa PREMIUM TIMES.

Fiye da kashi 50 cikin 100 na waɗanda aka yi fatali da su, sun yi aiki tare da Sanwo-Olu a zangon sa na farko. Yayin da shida tsoffin kwamishinonin sa ne, wasu kuma mashawartan sa ne na musamman a zangon farkon.

Daga cikin sunayen 39 da Gwamna Sanwo-Olu ya aika, Majalisa ta tantance 22 kaɗai, ta yi fatali da 17.

“Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Legas, Midashiru Obasa, ya ce tantancewar da yin fatali da wasu ya biyo bayan ƙa’idojin da Kwamitin Tantancewa na Majalisa ya yi aiki da su, a ƙarƙashin Bulaliyar Majalisa, Fatai Mojeed”.

Sai dai kuma sanarwar ba ta ce an ƙi tantance su ne saboda ƙoƙarin da Musulman Legas suka yi cewa Gwamna Sanwo-Olu ya naɗa kwamishinoni 39, amma 31 Kiristoci, 8 Musulmai.

Zargin Nuna Bambancin Addini Da Musulman Legas Ke Wa Gwamna Sanwo-Olu:

Farkon watan Agusta ne PREMIUM TIMES Hausa ta buga labarin cewa Ƙungiyar Malamai ta Jihar Legas sun ƙi yarda a naɗa Kwamishinoni 31 Kiristoci, 8 Musulmai:

Rikici ya na ƙara kunno kai tsakanin Kungiyar Malaman Addinin Musulunci ta Jihar Legas da kuma Gwamnatin Babajide Sanwo-Olu.

Duk da dai dama tun bayan hawan sa zango na farko su ke ƙorafi kan zargin fifita Kiristoci fiye da Musulmai a gwamnatin sa, sai ga shi kuma lamarin ya ƙara ƙarfi sosai tun bayan da Gwamna Sanwo-Olu ya fitar da sunayen Kwamishinonin Jihar Legas, ya aika wa Majalisar Dokokin Legas domin tantancewa.

Sai dai kuma tuni a wani taro da Haɗaɗɗiyar Ƙungiyar Malaman Legas mai suna JMT ta yi, ƙarƙashin jagorancin Shugaban Ansar-Ud-Deen na Ƙasa, Abdrahman Ahmad, sun yi fatali da sunayen kwamishinonin da Sanwo-Olu ya aika da su, tare da cewa gwamnan ya ƙara fitowa da nuna bambanci da ƙiyayya a fili ga Musulman Jihar Legas, waɗanda mafi yawan su ne ma su ka zaɓi APC, ba Kiristoci ne su ka zaɓe ta ba.

Ahmad Yahaya a ce ba tun yau Sanwo-Olu ke fifita Kiristoci a kan Musulmai wajen naɗe-naɗe ba, amma dai sunayen kwamishinonin da ya fitar a yanzu ya nuna lamarin gwamnan har ma akwai rainin wayo a ciki.

A cikin sunaye 39 da Gwamna Sanwo-Olu ya aika da su Majalisa, 8 kaɗai ne Musulmai, saura 31 Kiristoci.

Dama kuma kafin ƙungiyar ta malaman jihar Legas ta nuna fushin ta, sai da majalisar dokokin Legas ta maida sunayen, tare da yin ƙoƙarin cewa babu adalci a zaɓen kwamishinonin, domin an manta da wasu ƙananan hukumomin da gangan.

Daga cikin waɗanda suka halarci taron ƙungiyoyin addinin Musulunci na Legas, akwai Babban Mufti na CIO, Dhikrullah Shafi’i, Isiak Tejidini daga Rahmatu Islamiyyah, sai AbdulJaleel Olori-Aje na Ƙungiyar Ƙwararru Musulmai, sai Farfesa Isiaq Akintola wanda ya wakilci MURIC.

Sauran sun haɗa da Muhammad Basheer daga Zumratul Muhmineen, Isma’il Yusuf daga Ƙungiyar Musulmi ta Yankin Mainland, AbdulGafaar Muslideen daga Da’awah, Amina Muhammad daga Al-Furqan, da sauran wasu da dama.

“Kashi 60 bisa 100 na al’ummar Jihar Legas Musulmi ne. Kuma su ne suka tsaya tsayin daka su ka ha cewa an samu nasara a zaɓen da ya gabata. Domin Kiristoci ba su zaɓi wannan gwamnatin ba, saboda haushin Muslim-Muslim da aka yi a Shugaban Ƙasa da Mataimakin sa.” Cewar Ahmad.

“Mu na sanar da cewa gaba ɗaya ɗaukacin Musulmai na Jihar Legas mun yi fatali tare da rashin yarda da sunayen kwamishinonin da Gwamna Babajide Sanwo-Olu ya aika da su Majalisa.

“Mu na kira da janye sunayen, a sake duba lamarin, domin ba mu yarda duk da mu ne kashi 60 bisa 100 na jihar Legas ba, amma a ce wai za a naɗa Musulmai 8 Kwamishinoni, Kiristoci kuma waɗanda ba su zaɓi wannan gwamnatin sosai ba, a ce za a naɗa Kwamishinoni 31 a cikin su.”

Ya ce dama Gwamna Sanwo-Olu ya daɗe ya na nuna masu bambanci da addinanci, kuma sun sha yi masa ƙorafi, amma ba ya yi masu adalci.

A wannan karo, Ahmad ya ƙara da cewa ɗaukacin Musulman Jihar Legas ba su yarda da abin da gwamnan ke ƙoƙarin yi masu na rashin adalci da nuna fifita wani addini a gwamnatin sa ba.

“Babu wanda ya ba Musulmai ko sisi a lokacin zaɓe. Haka mu ka riƙa bi muna cewa a zaɓi APC da Gwamna Sanwo-Olu.”

Sai dai kuma a tattaunawar da Kakakin Yaɗa Labaran Gwamnan Jihar Legas ya yi da PREMIUM TIMES, Akosile ya jaddada cewa ba da gangan Sanwo-Olu ya ware wani addini ba. Ya ce ya bi tsarin cancanta ne da kuma raba-daidai da ɓangaren mata da na matasa.

Ya ce amma tunda ƙorafe-ƙorafe sun kunno kai, za a duba. “Domin a yanzu haka ana tuntuɓar shugabannin addinin Musulunci ɗin domin a yaye masu damuwar su. Kuma na tabbata daga ƙarshe abin da zai biyo baya, za a daidaita, babu wani ɓangaren da zai yi wani ƙorafi.” Inji shi.

Tags: AbujaLabaraiLegasMusulmaiNewsPREMIUM TIMESSanwo-Olu
Previous Post

‘Tu’ammali da muggan ƙwayoyi da ‘cutar damuwa’ na damun wasu Sojojin Najeriya’ – Lagbaja

Next Post

GA DAMA TA SAMU: KAMFANIN Jirgin sama na daukar daruruwar ma’aikata. Shin kana da sha’awar aiki da wannan Kamfani? Ga yadda za ka samu shiga

Ashafa Murnai

Ashafa Murnai

Next Post
GA DAMA TA SAMU: KAMFANIN Jirgin sama na daukar daruruwar ma’aikata. Shin kana da sha’awar aiki da wannan Kamfani? Ga yadda za ka samu shiga

GA DAMA TA SAMU: KAMFANIN Jirgin sama na daukar daruruwar ma'aikata. Shin kana da sha'awar aiki da wannan Kamfani? Ga yadda za ka samu shiga

Discussion about this post

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • ZARGIN KARKATAR DA KUƊAƊEN ALAWUS NA ƘANANAN SOJOJI: Kakakin Sojoji ya ƙaryata haka, ya yi karin haske a kai
  • RASHIN TSARO: Tinubu ya amince da sayo jiragen sama masu saukar ungulu 12 ga sojojin Najeriya – Lagbaja
  • A yi biris da Yadda Gwamnatin Zamfara ke siyasantar da matsalar tsaro – Minista
  • RA’AYIN PREMIUM TIMES: Rigimar Gwamnatin Tarayya da Ƙungiyar Ƙwadago abin damuwa ce matuƙa
  • Mutum sama da 7000 sun kamu da cutar diphtheria, cutar ta yi ajalin mutum 453

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.