Yayin da ake ci gaba da kallon-hadarin-kaji tsakanin ECOWAS da Sojojin Juyin Mulkin Jamhuriyar Nijar, ita ma Kungiyar Hadin Kan Afrika, AU, ta Kungiyar AU ta bai wa sojojin Nijar wa’adin kwana 15 su sauka, su kuma sojojin sun dunguri hancin ECOWAS.
AU ta gargardi sojojin da suka yi juyin mulkin cewa su tattara komatsan su cikin kwanaki 15 su koma barikin soja, su maida mulki a hannun farar hula.
A taron da Majalisar AU ta yi, mambobin kungiyar sun nuna matukar damuwar su dangane da juyin mulkin da aka yi a Jmahuriyar Nijar, wanda su ka ce ya kawo wa dimokradiyya koma baya, ya gurgunta tsaron kasar, kuma ya kawar da Nijar daga turbar wanzuwar kwaciyar hankali da ma Nahiyar Afrika baki daya.
AU ta kara tabbatar da cewa ba za ta taba amincvewa da mulkin soja a cikin Nahiyar ba, kuma ta nemi a gaggauta sakin shugaban da suka hambarar, Mohammed Bazoum.
Haka kuma AU ta hori sojojin Juyin Mulki su mutunta ‘yancin jama’a, lafiyar Bazoum da kuma mutuncin sa.
Mun Fi Karfin ECOWAS Ta Zare Mana Idanu – Sojojin Nijar:
A ranar Asabar kuma Sojojin Juyin Mulkin Nijar su ka gargadi ECOWAS cewa ba za su yi sassaauci ga duk wani yunkurin yin amfani da karfin soja a kan sabuwar gwamnatin ta su ba.
Sun ce sun fahimci take-taken ECOWAS shi ne yin amfani da karfin soja a kan Nijar, ta hanyar hada kai da AU, har da kasashen da ba ECOWAS ba. Haka Amadou Abdramane ya bayyana.
Discussion about this post