• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Ƴan sanda sun damke wasu abokai ƴan kungiyar matsafa dake tsafi da kawunan mutane a Ilori

    Yadda ƴan sanda suka kama Ibrahim da ya yi garkuwa da Fatima, ya ƙarɓi kuɗi kuma ya yashe ta a Zariya

    Kotu ta kori gwamna Sule na Nasarawa, ta ce PDP ce ta yi nasara a zaɓen gwamna

    Kotu ta kori gwamna Sule na Nasarawa, ta ce PDP ce ta yi nasara a zaɓen gwamna

    Ku fito ku ceci mutanen jihar Kaduna kamar yadda kuka yi a zaben majalisun Tarayya da na sanatoci – Isah Ashiru

    An yi mana kwange a hukuncin kotu, za mu daukaka kara – Ashiru

    SSS

    TAKE HAƘƘIN ƊAN ADAM: Yadda SSS suka riƙa faffalla min mari, suka ja ni ƙasa girrrr, don kawai na ce su bi doka – Lauya Ogbankwa

    Muna ƙarancin malamai, a janye dokar hana ɗaukar sabbin malamai da gwamnatin tarayya ta ƙaƙaba – Jami’ar ABU

    Muna ƙarancin malamai, a janye dokar hana ɗaukar sabbin malamai da gwamnatin tarayya ta ƙaƙaba – Jami’ar ABU

    TONON ASIRI: An kama wani Dagaci cikin gungun mahara a lokacin batakashi da ‘Yan sanda

    ‘Yan bindiga sun kashe mutum shida a Kaduna

    Almajirai

    UNICEF ta saka Almajirai sama da 20,000 cikin rajistar tsarin agaza wa marasa karfi a Katsina

    Majalisar Tarayya ta ce a soke ƙarin kuɗin makaranta da aka yi wa ɗaliban jami’o’i da na Kwalejojin Gwamnatin Tarayya

    KALUBALEN DA KE GABAN MAJALISAR WAKILAI TA ƘASA: Gaganiya da matsalar raɗaɗin tsadar rayuwa, matsalar tsaro da sauran su da ake fuskanta a kasa

    Yadda sojojin sama sun ragargaza sansanonin ‘yan bindiga a jihohin Katsina, Zamfara, Sokoto da Kaduna

    RASHIN TSARO: Tinubu ya amince da sayo jiragen sama masu saukar ungulu 12 ga sojojin Najeriya – Lagbaja

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    Hukumar CAF za ta binciki yadda mahaifiyar ɗan wasa ta mutu cikin 1986, shi kuma ya ce atabau cikin 1990 ta haife shi

    A karo na Uku, Moroko za ta ɗauki baƙuncin gasar cin kofin kwallon ƙafa na nahiyar Afrika a Janairun 2025

    NFF ta sake nada Chris Danjuma a matsayin kocin Falconets

    NFF ta sake nada Chris Danjuma a matsayin kocin Falconets

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    JERIN SUNAYE: Jami’o’i 51 da ba za su dauki dalibin da ya ci kasa da maki 180 a jarabawar JAMB ba

    TSARIN BAI WA ƊALIBAI RAMCE: Abubuwan da suka wajaba ɗalibai da iyaye su sani

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Ƴan sanda sun damke wasu abokai ƴan kungiyar matsafa dake tsafi da kawunan mutane a Ilori

    Yadda ƴan sanda suka kama Ibrahim da ya yi garkuwa da Fatima, ya ƙarɓi kuɗi kuma ya yashe ta a Zariya

    Kotu ta kori gwamna Sule na Nasarawa, ta ce PDP ce ta yi nasara a zaɓen gwamna

    Kotu ta kori gwamna Sule na Nasarawa, ta ce PDP ce ta yi nasara a zaɓen gwamna

    Ku fito ku ceci mutanen jihar Kaduna kamar yadda kuka yi a zaben majalisun Tarayya da na sanatoci – Isah Ashiru

    An yi mana kwange a hukuncin kotu, za mu daukaka kara – Ashiru

    SSS

    TAKE HAƘƘIN ƊAN ADAM: Yadda SSS suka riƙa faffalla min mari, suka ja ni ƙasa girrrr, don kawai na ce su bi doka – Lauya Ogbankwa

    Muna ƙarancin malamai, a janye dokar hana ɗaukar sabbin malamai da gwamnatin tarayya ta ƙaƙaba – Jami’ar ABU

    Muna ƙarancin malamai, a janye dokar hana ɗaukar sabbin malamai da gwamnatin tarayya ta ƙaƙaba – Jami’ar ABU

    TONON ASIRI: An kama wani Dagaci cikin gungun mahara a lokacin batakashi da ‘Yan sanda

    ‘Yan bindiga sun kashe mutum shida a Kaduna

    Almajirai

    UNICEF ta saka Almajirai sama da 20,000 cikin rajistar tsarin agaza wa marasa karfi a Katsina

    Majalisar Tarayya ta ce a soke ƙarin kuɗin makaranta da aka yi wa ɗaliban jami’o’i da na Kwalejojin Gwamnatin Tarayya

    KALUBALEN DA KE GABAN MAJALISAR WAKILAI TA ƘASA: Gaganiya da matsalar raɗaɗin tsadar rayuwa, matsalar tsaro da sauran su da ake fuskanta a kasa

    Yadda sojojin sama sun ragargaza sansanonin ‘yan bindiga a jihohin Katsina, Zamfara, Sokoto da Kaduna

    RASHIN TSARO: Tinubu ya amince da sayo jiragen sama masu saukar ungulu 12 ga sojojin Najeriya – Lagbaja

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    Hukumar CAF za ta binciki yadda mahaifiyar ɗan wasa ta mutu cikin 1986, shi kuma ya ce atabau cikin 1990 ta haife shi

    A karo na Uku, Moroko za ta ɗauki baƙuncin gasar cin kofin kwallon ƙafa na nahiyar Afrika a Janairun 2025

    NFF ta sake nada Chris Danjuma a matsayin kocin Falconets

    NFF ta sake nada Chris Danjuma a matsayin kocin Falconets

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    JERIN SUNAYE: Jami’o’i 51 da ba za su dauki dalibin da ya ci kasa da maki 180 a jarabawar JAMB ba

    TSARIN BAI WA ƊALIBAI RAMCE: Abubuwan da suka wajaba ɗalibai da iyaye su sani

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

SHARI’AR ZAƁEN SHUGABAN ƘASA: Peter Obi ya yi wa kotu saukalen lodin takardun sakamakon zaɓe kwafe 18,000 daga IReV

Ashafa MurnaibyAshafa Murnai
June 15, 2023
in Babban Labari
0
SHARI’AR ZAƁEN SHUGABAN ƘASA: Peter Obi ya nemi kotu ta ɗage sauraren shari’ar da ya maka Tinubu

Ɗan takarar shugaban ƙasa. A zaɓen 2023 a ƙarƙashin jam’iyyar LP, Peter Obi, ya ci gaba da danƙara wa wa Kotun Ɗaukaka Ƙararrakin Zaɓen Shugaban Ƙasa tulin hujjojin da ya ke neman kafawa domin neman yin nasara a kotu.

A ci gaba da zaman ranar Alhamis, Peter Obi ya yi wa kotu saukalen lodin takardun sakamakon zaɓe kwafe 18,000 daga IReV, da ya ce dishi-dishi su ke, ba su karantuwa.

Wani ƙwararren masanin manhaja da laƙanin sirrin kwamfuta ne ya bayar da wannan shaida cewa shafukan 18,000 duk ba a iya ganin sakamakon zaɓen da ke cikin su, saboda shafukan duk garara-garara su ke.

Lauyan Peter Obi, Onyechi Ikpeazu ne ya gabatar da mai bayar da shaidar, mai suna Erik Uwadiagwu, wanda ya yi nazarin ‘data’ ɗin bayanan sakamakon da ke cikin Manhajar Rumbun Tattara Sakamakon Zaɓe na IReV, na INEC.

Uwadiagwu, wanda Farfesa ne a darasin lissafi, a Jami’ar Nnamdi Azikwe, Awka, Jihar Anambra, ya bayyana a gaban kotun bisa gayyatar Obi, domin bayar da shaida.

Kafin ya fara bayani sai da ya yi rantsuwar kaffara da Kwansitushin, a matsayin babban mai bayar da shaida na Peter Obi.

Ya ce ya yi nazarin shafukan IReV 18,000 daga Manhajar Rumbun Tattara Sakamakon Zaɓe, wanda hotunan kwafen sakamakon zaɓe ne INEC ke lodawa a ciki, daga Na’urar Tantance Masu Shaidar Rajistar Zaɓe, wato BVAS.

PREMIUM TIMES ta buga labarin yadda Peter Obi ya jibge wa kotu rahotannin Manhajar Rumbun IReV na INEC, ya ƙara matsa-ƙaimin ƙure Tinubu.

Ɗan takarar zaɓen shugaban ƙasa na jam’iyyar LP, Peter Obi, ya ci gaba da damƙa wa kotu bayanan hujjojin da ya ke bayarwa domin kotu ta ƙwace nasarar da INEC ta ce Bola Tinubu na APC ya yi ta ba shi, ko kuma a sake zaɓe ɗungurugum.

A ranar Talata ce Obi ya gabatar wa kotu rahotannin da INEC ta fitar dangane da Manhajar Rumbun Tattara Sakamakon Zaɓe (IReV), a Abuja.

INEC dai tun kafin zaɓe ta yi alƙawarin cewa za ta watsa sakamakon zaɓe daga BVAS zuwa Manhajar Rumbun Tattara Sakamakon Zaɓe (INEC) yadda kowa zai shiga manhajar, wato ‘portal’ don ya ga kwafe-kwafen sakamakon zaɓen kowace rumfar zaɓe, bayan kammala zaɓe. Amma ba ta yi hakan ba.

Wannan rashin cika alƙawarin da INEC ta yi ya harzuƙa dama a ƙasar nan da masu sa-ido.

Hakan na daga cikin manyan dalilan da su ka sa Peter Obi ya garzaya kotu, ya yi zargin an yi maguɗi a zaɓen.

Obi ya yi zargin INEC ta haɗa baki da Tinubu an yi masa maguɗi.

A ci gaba da sauraren ƙara a ranar Talata, lauyan Obi mai suna Peter Afoba, wanda Babban Lauya ne, ya gabatar wa kotu rahoton Manhajar IReV daga jihohi biyar da su ka haɗa da Ribas, Akwa Ibom, Ekiti, Ogun da kuma Adamawa.

Ya shaida wa kotu cewa dukkan rahotannin sai da INEC ta tabbatar da cewa ita ce ta fitar da shi.

Afoba ya shaida wa kotu cewa rahotannin akwai wasu daga ƙananan hukumomi 21 na Adamawa, 20 daga Ogun, 16 daga Ekiti, 19 daga Ribas da kuma 25 daga Akwa Ibom.

Saɓanin yadda INEC ta bayyana, wani nazari da PREMIUM TIMES ta yi ya nuna cewa LP ce ta lashe zaɓe a Jihar Ribas, ba Tinubu ba, kamar yadda INEC ta bayyana.

Sai dai lauyan INEC Kemi Pinheiro shi da lauyan APC da na TInubu duk sun ƙi yarda a gabatar da kwafen bayanan. Amma duk da haka kotu ta karɓa.

Wani lauyan Obi mai suna Audu Onuga, ya ƙara maka wa kotu kwafe-kwafen bayanan ƙoƙarin ganin an haramta wa Tinubu wasiƙa zaɓen 2023.

Ɗan takarar shugaban ƙana na LP a zaɓen 2023, Peter Obi, ya ƙara danƙara wa Kotun Ɗaukaka Ƙararrakin Zaɓen Shugaban Ƙasa wasu kwafe-kwafen bayanan da ya ce ke da alaƙa da rashin sahihancin zaɓen shugaban ƙasa, wanda INEC ta shirya a ranar 25 ga Maris, 2023.

Kwafen takardun bayanan dai duk sun ƙunshi sakamakon zaɓuɓɓuka da kuma rahotannin da INEC ta yi dangane da yadda aka gudanar da zaɓen shugaban ƙasa.

Obi ya maka APC, Bola Tinubu, Kashim Shettima da INEC a kotu, inda ya ke ƙalubalantar nasarar da INEC ta ce Tinubu na APC ya yi.

Bayanan da Peter Obi ya maka wa kotu a ranar Talata, ta hannun lauyan sa kuma (SAN), Peter Afoba, sun haɗa da fam-fam masu lamba EC40GPU, EC40G1 da kuma rahotannin da INEC ta riƙa bayarwa bayan kammala zaɓen.

Peter Obi ya maka wa kotu fam mai lamba EC40GPU har guda 45 daga ƙananan hukumomi 10 na Jihar Neja, sai wasu 23 daga ƙananan hukumomi bakwai na Jihar Osun.

Sannan akwai wasu 17 daga ƙananan hukumomi uku na jihar Edo, sai kuma fam 52 daga ƙananan hukumomi biyar na Jihar Sokoto.

Peter Obi har ila yau ya maka wa kotu fam-fam mai lamba EC40G guda 15 daga ƙananan hukumomi takwas na Jihar Osun, sai wasu fam-fam masu lamba EC40G1 daga ƙananan hukimomi 12 na jihar Edo.

Akwai kuma fam-fam 15 masu lamba EC40G daga ƙananan hukumomi huɗu na jihar Sokoto, sai wasu tara daga ƙananan hukumomi biyu na Jihar Sokoto, masu lamba EC40G1.

Peter Obi ya kuma bai wa kotu kwafen rahotannin da INEC ta yi dangane da yadda zaɓen shugaban ƙasa ya kaya a Neja, Edo, tare da zargin an tafka maguɗi lokacin gudanar da zaɓen.

Ya kuma maka wa kotu rahoton INEC kan Manhajar Tattara Sakamakon Zaɓe (IRev) na ƙananan hukumomi 21 daga jihar Adanawa, wasu kuma daga Ogun, wasu daga Ekiti, Ribas da Akwai Ibom.

Fam EC40G: Fam ne mai ɗauke da bayanan adadin ƙuri’un wuraren da ba a yi zaɓe ba, ko aka soke zaɓen.

Fam EC40GPU: Mai ɗauke da bayanan lokacin da aka yi zaɓe a rumfar zaɓe.

Sai dai lauyoyin Tinubu, INEC da na APC da Kashim Shettima duk nuna wa kotu cewa ba su goyi bayan Obi ya gabatar da kwafe-kwafen bayanan a kotu ba.

Kotun dai a ƙarƙashin jagorancin sauran alƙalai huɗu, Haruna Tsammani ya ɗage zaman ta zuwa washegari Laraba.

Tags: AbujaHausaKashim ShettimaLabaraiNajeriyaNewsPeter ObiPREMIUM TIMES
Previous Post

AN GUDU BA A TSIRA BA: ‘Baban Aisha’, mai maganin gargajiya ya shiga hannu

Next Post

Dokar Baiwa Daliban Najeriya Bashin Kuɗin Karatu kan iya Durkushe Ilimi a Arewacin Najeriya, Daga Ahmed Ilallah

Ashafa Murnai

Ashafa Murnai

Next Post
Islamic school for girls and young women in Kano

Dokar Baiwa Daliban Najeriya Bashin Kuɗin Karatu kan iya Durkushe Ilimi a Arewacin Najeriya, Daga Ahmed Ilallah

Discussion about this post

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • Yadda ƴan sanda suka kama Ibrahim da ya yi garkuwa da Fatima, ya ƙarɓi kuɗi kuma ya yashe ta a Zariya
  • Kotu ta kori gwamna Sule na Nasarawa, ta ce PDP ce ta yi nasara a zaɓen gwamna
  • Gwamnatin Tinubu ta sanar da dakatar da harajin (VAT) kan man dizal na tsawon watanni 6
  • Matsayar da aka cimma a taron Gwamnatin Tarayya, NUC da TUC – Minista Idris
  • ‘Gyaran Najeriya sai a hankali, miji na ba da rauhanai ya ke aiki ba’ – Remi Tinubu

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.