Tsohon Shugaban Ƙasa na mulkin soja, Janar Ibrahim Babangida mai ritaya, ya hori ‘yan siyasa cewa su yi amfani da ribar zaɓen 12 ga Yuni, 1993 domin su ƙara wa daɓen dimokraɗiyya makuba.
Babangida ya yi wannan bayani a Minna, yayin ganawar sa da Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN), tattaunawar da su ka yi a kan dimokraɗiyya.
“Ribar zaɓen ranar 12 ga Yuni, 1993, zaɓe na shugaban ƙasa, ina ganin har yanzu ‘yan siyasa ba su yi amfani da wannan ribar ba a zaɓukan da su ka biyo na 12 ga Yuni ɗin.
“An yi ittifaƙin cewa shi ne zaɓe mafi sahihanci da inganci a tarihin zaɓukan da aka yi a ƙasar nan. Amma kuma har yau ‘yan siyasa sun ƙi amfani da darussan da wannan sahihin zaɓe ya koyar.
“Ku tuna shi ne zaɓen da ‘yan Najeriya su ka yi tururuwar fita domin su zaɓi shugabannin su.”
Da Babangida ke magana ta bakin Kakakin Yaɗa Labaran Babangida, Kasim Afegbua, Babangida ya ce, “A yanzu dabanci da tashin hankula sun yi yawa.”
Babangida ya nuna rashin jin daɗin yadda a shekarun da su ka gabata zuwa yau, a lokacin kowane zaɓe za ka ga masu jefa ƙuri’a sai raguwa su ke yi a lokutan zaɓe.
“Kamata ya yi a ce zaɓen 12 Ga Yuni ya ƙara zaburar da jama’a tururuwar fita su jefa ƙuri’a dandazo-dandazo, ta yadda dimokraɗiyyar za ta ƙara karsashi a idanun jama’a. Amma abin takaici yawan masu jefa ƙuri’a sai raguwa su ke yi, maimakon a ce su na ƙaruwa sosai da sosai.”
Discussion about this post