Kwamitin Majalisar Tarayya mai lura da Sufurin Jiragen Sama, ya yi kira ga Gwamnatin Tarayya ta gaggauta soke kamfanin Zirga-zirgar Jiragen Najeriya, Nigeria Air, wanda aka ƙaddamar cikin satin da tsohon Shugaban Ƙasa, Muhammadu Buhari ya sauka kan mulki.
Kwamitin ya kuma yi kira a gaggauta kamawa tare da garƙame dukkan masu hannu a gidoga da rufa-rufar ƙaddamar da Nigeria Air, wanda majalisa ta ce damfara ce kawai ba wani kamfanin sufurin jirage ba.
An cimma yarjejeniyar amincewa a kira gwamnatin tarayya ta dakatar da Nigeria Air, a lokacin da su ka yi taro da wasu jami’an gwamnati masu ruwa da tsaki a fannin sufurin jiragen sama, a Majalisar Tarayya, Abuja.
Shugaban Kwamiti Nnolim Nnaji, ɗan PDP daga Enugu ne ya karanta matsayar da su ka ɗauka yayin taron.
Waɗanda su ka halarci taron sun haɗa da Ƙungiyar Masu Jiragen Sama ta Najeriya (AON), wakilan Ma’aikatar Harkokin Sufuri ta Ƙasa da sauran su.
Tsohon Ministan Harkokin Sufuri a lokacin mulkin Buhari, wato Hadi Sirika ne ya ƙaddamar da jirgin, wanda daga baya aka haƙƙace cewa holoƙo ne, kuma damfara ce kawai.
Discussion about this post