Gwamnan Jihar Kano, Abdullahi Ganduje ya bada sanarwar cewa gwamnonin jam’iyyyar APC sun yanke shawarar amincewa su zaɓi shugaban majalisar dattawa daga yankin Kudu maso Kudu.
Dama kuma a baya sun ce ko dai ya shugaban majalisar dattawa ɗin ya fito daga Kudu maso Gabas ko kuma ya fito daga Kudu maso Kudu.
Sun kuma yarda cewa muƙaman shugaban masu rinjaye da mataimakin masu rinjaye da kuma bulaliyar majalisa, a bayar da su ga ‘yan takarar da aka roƙa su ka janye.
Sai dai kuma a cikin wani bidiyo da aka datso daga gidan talabijin na AIT, an nuno Ganduje ya tabbatar da cewa gwamnonin APC sun amince a zaɓi tsohon gwamnan jihar Akwa Ibom, Godswill Akpabio ya zama Shugaban Majalisar Dattawa, domin ɗan yankin Kudu maso Kudu ne.
A cikin bidiyon an nuno Ganduje tare da wasu gwamnoni ciki har da Ben Ayade na Kuros Riba a wurin taro da wasu mutane.
Ganduje ya ƙara tabbatar da cewa babu abin da zai canja tsarin raba muƙaman majalisar dattawa da na majalisar tarayya zuwa shiyya-shiyya, kamar yadda su gwamnonin su ka tsara.
“Shugaban Majalisar Dattawa mun yarda a bai wa ɗan Kudu maso Kudu. Kuma tsohon gwamnan Akwa Ibom, Sanata Godswill Akpabio mu ke so a bai wa.” Inji Ganduje.
Discussion about this post