Hukumar EFCC ta bayyana cewa ta na binciken Gwamna Bello Matawalle na Zamfara, bisa zargin sa da karkatar da naira biliyan 70 daga dukiyar al’ummar Zamfara.
Kakakin Yaɗa Labaran EFCC, Osita Nwajah ne ya bayyana haka, a ranar Alhamis, lokacin da ya ke yi wa manema labarai jawabi.
Ya ce, ” maganar da ake ciki kan Gwamna Matawalle ita ce, ana binciken sa kan karkatar da naira biliyan 70 a tsari na bayar da kwangilar bogi.”
EFCC ta bayyana haka, kwana ɗaya bayan Matawalle ya nemi Shugaban EFCC Bawa ya sauka a bincike shi, saboda a cewar sa, shi ma ɗan cuwa-cuwa ne.
Nwajah ya ce “Matawalle ya karkatar da kuɗaɗen waɗanda aka karɓo matsayin lamuni daga wani banki, domin a yi wasu ayyukan raya jiha da karkara, amma sai aka karkatar da kuɗaɗen domin amfanar gwamnan. An karkatar da kuɗaɗen ga wasu makusantan Matawalle, da sunan kwangila, amma ba a yi kwangilolin ba.”
“Sama da kamfanoni 100 sun karɓi kaso daga cikin kuɗaɗen, amma babu shaidar sun yi ayyuka da kuɗaɗen.”
“Wasu da su ka karɓi kuɗaɗen, ai EFCC ta gayyato su. Sun bayyana yadda Matawalle ya tilasta su maida masa kuɗaɗen ta hannun wasu yaran sa, bayan sun canja su zuwa Dalar Amurka.”
EFCC ta ce waɗanda aka tura wa kuɗaɗen sun tabbatar mata cewa ba su yi wa Jihar Zamfara aiki ko da na gina kwalbati guda ɗaya ba.
“An riƙa maida wa Matawalle kuɗaɗen ta hannun Kwamishinan Kuɗaɗe na Zamfara da Kwamishinan Harkokin Ƙananan Hukumomi.” Inji EFCC.
“Wani ɗan canji a Zamfara ya karɓi naira biliyan 6 da sunan biyan kuɗin kwangila, amma ko kwalbati bai yi ba. Ɗan canjin a Abuja ya ke.”
Discussion about this post