Kashe-kashen da su ka afku a ranar Talata a Ƙaramar Hukumar Mangu, an tabbatar da salwantar rayuka 85 a ƙauyukan Fungzai da Kubwat.
Shugaban Ƙungiyar Ƙabilar Mwaghavul na Ƙasa, Joseph Gwankat ne ya bayyana haka, lokacin da ya ke zantawa da ‘yan jarida, a ranar Laraba.
Ya gaba da manema labarai ɗin ne bayan taron da aka yi a fadar Basarake Mishkcham Mwaghavul na Mangu, John Hirse.
Har yanzu dai ‘yan sanda ba su fito sun bayyana adadin waɗanda aka kashe ba.
Shi kuma Gwankat ya ce ana ci gaba da neman mutanen da har yanzu ba a ji ɗuriyar su ba tukunna a cikin yankunan biyu da aka yi mummunan kisan.
Ya ce an kai wa ƙauyuka da dama hari, kuma duk kusan a lokaci a lokaci ɗaya.
Mazauna yankunan dai na zargin cewa makiyaya ne su ka yi kisan, kuma su ka riƙa banka wa bukkoki wuta da kuma lalata amfanin gona.
A lokacin taron da aka yi a fadar Basaraken Mangu, an ga mata sun fito har fadar su na cike da nuna fushi su na zanga-zangar lumana.
Cikin waɗanda su ka halarci taron akwai Mataimakin Gwamnan Filato, Soni Tyoden, shugabannin hukumomin tsaro, dagatai da jami’an gwamnati daban-daban.
Hirse, Shugaban Ƙaramar Hukuma da Hakimai sun roƙi a ƙara yawan jami’an tsaro a yankunan.
Zuwa lokacin haɗa labarin dai an binne gawarwaki 57 a safiyar Laraba ɗin nan.
Discussion about this post