Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya bayyana cewa ya kammala shiri tsaf domin komawa Daura ya ci gaba da kula da Shanun da saurai dabbobin sa wanda ya kai shekara 8 rabon sa da su.
Buhari ya bayyana haka ne a jawabin ban kwana da yayi wa ministoci da jami’an gwamnati wanda suka halarci taron majalisar zartaswa ta karshe wanda Buhari zai shugabanta a matsayin sa na shugaban Najeriya.
” Tun 2015 ban sako komawa ga Dabbobi na in kula da su ba, saboda aikin gwamnati. Amma yanzu na kosa in in yi sallama da Abuja in koma gida Daura domin ci gaba da kula da su.
” Bayan haka ina so in roke ku musamman wadanda ba za su kasance cikin gwamnati mai zuwa ba da su ci gaba da bada gudunmawar su domin ci gaban kasa da kuma jam’iyyar APC.
A karshe ya roki abokan aikin sa da su rika garzayowa Daura ana gaggaisawa.
” Ina rokon ku duka ku rika zuwa muna gaggaisawa a garin Daura, duk da dai na san yanzu Dauran za ta yi muku nisa saboda ba nine shugaban kasa ba kuma.”
” Fata ne shine Allah ya sa a fadi Alkhairi akan mu duka a duk lokacin da aka ambaci sunayen mu bayan mun sauka daga kan mulki.
Discussion about this post