Masu iya magana na cewa, ruwa abokin aiki. Wasu kuma su ce abokin rayuwa. Ruwa abu ne mai matukar mahimmanci ga rayuwar hallittu gaba daya.
Wannan yasa mutum ke bukatar tsaftataccen ruwa don gudanar da ayyukan yau da kulum kamar sha, girki, wanki, wanka da sauransu.
Sai dai a duk lokacin da aka samu rashin ruwa wadatacce, al’umma kan shiga halin tagayyara, inda komai na su kan dagule,su rasa inda zasu sa kawunnan su.
Wannan matsala na karancin ruwa kan shafi yara, manya,maza da mata, musamman a lokacin rani,kafin damina ta fadi. Kadan daga cikin matsalolin rashin ruwa sun hada da: rashin zuwa makaranta ga yara,rashin yin girki,wanki a gidaje,yawaitar cuttutuka kamar su typhoid ,kwalara da sauransu, sakamakon rashin samun tsaftataccen ruwa. Idan muka waiwaya baya,daga cikin kudurorin gwamnatin jihar Kaduna karkashin gwamna Nasir El- Rufai, shine na samar da tsaftataccen ruwan sha a duk fadin jihar, inda ya dau aniyar kashe bakan gizon da ke shanye ruwan Zariya,ta hanyar ci gaba da aikin madatsar ruwan Zariya da aikin yaki ci ya kicinye wa tsawon shekaru.
Duk da kudaden da aka zuba a wannan bagaren kimanin naira miiyan 24, tareda shimfida bututu a wurare cikin garin Zariya, wurare da ke zaton ruwa zai samu na nan kandas.
Abin takaicin shine :wasu wuraren da ke samun ruwa ada,a yanzu da aka sauya bututun sun daina samun ruwa tsawon shekaru, kamar wani yanki na tudun wadan Zariya. A yayin da muke zantawa da wasu al’umma a cikin garin Zariya, sun shaida min yadda suke tagayyara a duk lokacin da rani yayi nisa, inda rijiyoyi kekafewa, burtsatse ke lalacewa saboda tsabar dibar ruwa.
Mallam Isa dake zaune a cikin ganuwa,ya shaida min yadda suke dogara da masu borehole, wanda suke kunna musu ruwa don samun na amfanin gida.
Malamin ya kara da cewa,idan kuma akayi rashin sa’a ba wutan Nepa, tohsai dai su dogara da sayen ruwa wurin ‘yan garuwa a farshi mai tsada dukjarka.A cewar sa, ‘kana fama da kudin abin masarufi, ga kuma Karin na siyan ruwa’.
Shima wani matashi mai suna Ibrahim a filin mallawa,tudun wadan Zariya, ya koka kan matsalar ruwa.Ya nuna irin fargaban zuwan lokacin rani da suke, sakamakon konewa da rijiyar su ke yi,ruwa pampon kuma bai zuwa yadda ya kamata.Ibrahim ya bayyana yadda suke fita tun sassafe wurin neman ‘yan garuwa,inda yace wani lokaci kafin ka karaso gida, wasu sun kwashe kana kallo kiri-kiri, wato dai ‘survival of the fittest’. Hulaira, wata dattijuwa dake zaune a makwalla bakin kasuwan Zariya ta bayyana yadda take fita da ‘yan jikokin ta marayu da assalatu wurin neman ruwan aikin gida.Tace a matsayin ta na talaka tubus, ba zata iya sayen jarkan ruwa ba,sai dai su rinka bin gidajen da rijiyarsu bai kone ba, ko gidan wani bawan Allah mai bada ruwan borehole ko rijiyar shi bayan an gama sallar asuba, ko burtsatsen da gwamnati ta sa (in bai lalace ba). Hulaira tace wani lokaci takan rasa sallar asuba akan lokaci, saboda gudun kar a cire mata bokiti daga layi.Toh amma, Hausawa na cewa; ‘In anbi ta barawo, to a bi ta mabi sawu’. kuma ‘inbera da sata, daddawa ma tana da wari’.
Ma’ana,in har an ga gazawar gwamnati wurin samar da isashshen ruwa,toh su ma Jama’a akwai rashin tattala kayan da gwamnati tayi musu. Misali, Hukumar samar da ruwan sha da tsaftar muhalli ta Jihar Kaduna (RUWASSAS),ta himmatu wurin samar da pampuna masu amfanida hasken rana a wasu yan kuna na garin Zariya. Sukan kafa tanki mai amfani da hasken rana da kan pampo shida a wuri guda,sannan sai su ja ruwan zuwa lunguna da sakunan cikin unguwa don jama’a su samu saukin samun ruwan amfanin yau da kullum.Tabbas wanna hubbasa ya samar da ruwa ga al’umma,kuma har yanzu gawuraren da suka tattala shi,suna mora.
Sai dai akwai wurare da yawa da muka kai ziyara,inda wasu pampunan an kakkarya kansu, wasu bama sandan pipe din gaba daya da dai sauran matsaloli da rashin kishi da tattali kan jawo. Unguwannin da suka yi shakwalatin bangaro da pampuna, suka barma yara suyi yadda suke so, na cikin halin ha’ula’i saboda rashin ruwa a wannan lokacin ranin.Da wannan nake kira ga al’umma da su rike kayan da gwamnati tasa musu don amfanin su da muhimmanci don gudun shiga halin kaico.
Khadijah Sulaiman.Khadijahsulaiman93@gmail.com
Discussion about this post