Shugaba Muhammadu Buhari ya bayyana Matatar ta wadda ya buɗe a Legas, cewa za ta sauya ci gaba da tattalin arzikin Najeriya ɗungurugum, kuma za ta bunƙasa harkokin fetur, ba a Najeriya kaɗai ba, har ma Afrika baki ɗaya.
Shugaba Buhari ya buɗe Matatar Fetur ɗin a Ijebu-Lekki, Legas, wadda ake kyautata wa yaƙini da tabbacin wadatar da Najeriya fetur ɗin da ta ke buƙata a kullum, har ma a riƙa fitarwa ƙasashen waje.
Sanarwar da Kakakin Shugaban Ƙasa ya fitar, Femi Adesina ya ce Buhari ya yi furucin ne a lokacin da ya ke buɗe matatar fetur ɗin, a ranar Litinin.
Shugabannin ƙasashen Ghana, Togo, Nijar da Sanagal duk sun halarta. Chadi ma ta aiko wakilin shugaban kasar su ya halarta.
“Wannan katafariyar masana’anta da mu ke buɗewa a yau, babban misali ne na abin da za mu iya cimma idan aka ƙarfafa wa masu zuba jari guiwa, ta hanyar bunƙasa kasuwancin su domin haɓɓaka tattalin arzikin Najeriya.” Inji Buhari.
“Ina da yaƙinin cewa wanda zai gaje ni, Zaɓaɓɓen Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, zai ci gaba da inganta tattalin arzikin ƙasa ta hanyar ƙarfafa wa manyan masu zuba jari, domin tattalin arziki ya bunƙasa.
“Ina matukar farin ciki zan bar tattalin arzikin Najeriya a hannun wanda ya dace kuma ya cancanta ya kula da shi sosai da sosai.”
Buhari ya jinjina wa Aliko Ɗangote, wanda ya kafa matatar da za ta iya tace ganga 650,000 a
Kowace rana.
Daga nan ya shawarci sauran manyan ‘yan kasuwa da masu zuba jari su kwaikwayi irin hoɓɓasar da Dangote ya yi.
Discussion about this post