Alamomi masu ƙarfi kuma tabbatattu na nuna cewa Zaɓaɓɓen Shugaban Ƙasa, Bola Tinubu ya amunce Honorabul Tajuddeen Abbas daga Jihar Kaduna ya zama Kakakin Majalisar Wakilai ta Ƙasa, wato Majalisar Tarayya.
Haka kan kuma ya amince Ben Kalu daga Abia ya zama Mataimakin Kakakin Majalisar Tarayya.
Idan hakan ta tabbata, to yankin Arewa ta Tsakiya ya tashi a cikin ‘yan-kalar-dangi kenan, ta yadda dukkan muƙamai shida bai samu ko ɗaya ba.
Tinubu ya amince da Abbas a wani taron da aka yi a ranar Juma’a da rana, a gidan da Gwamnatin Tarayya ta zaunar da Zaɓaɓɓen Shugaban Ƙasa, wato Defence House, da ke Maitama, Abuja.
Ben Kalu, wanda ɗan majalisa ne daga Jihar Abiya, a yankin Kudu maso Gabas, an ɗauko shi ne domin a saisaita giɓin yankin na su.
Alamomi kuma sun nuna cewa Tinubu ya amince tsohon Gwamnan Jihar Akwa Ibom, Godswill Akpabio ya kasance Shugaban Majalisar Dattawa, shi kuma Barau Jibrin daga Kano ya zama mataimakin sa.
An ɗauki Barau daga Arewa maso Yamma, yankin da Shugaban Ƙasa mai barin gado, Buhari ya fito.
Tunda Shugaba ya fito daga Kudu maso Yamma, mataimakin sa daga Arewa maso Gabas, Kakaki daga daga Arewa maso Yamma, Shugaban Majalisar Dattawa daga Kudu maso Kudu, sauran muƙamai da su ka rage kuma za a raba su cikin sauran shiyyoyi kenan.
A kula cewa Mataimakin Shugaban Majalisar Tarayya zai fito daga Kudu maso Gabas kenan, idan aka tafi a kan wannan yarjejeniya.
Takarar Shugabancin Majalisar Tarayya: ‘Ba Zan Janye Wa Kowa Ba’: Hasalallen ɗan takara daga Arewa ta Tsakiya:
Wani ɗan takara daga Arewa ta Tsakiya da ya nemi a sakaya sunan sa, ya shaida wa wakilin mu cewa ba fa zai janye wa kowa takarar da ya ke yi ba.
Ya ce ya tuntuɓi shugabannin LP da Rabi’u da Gwamna Bala Mohammed na Bauchi da wasu, kuma duk sun ba shi tabbacin zai yi nasara a zaɓen Kakakin Majalisa da za a yi a ranar 13 Ga Yuni.