Jam’iyyar APC Reshen Jihar Ribas ta nesanta kan ta daga ziyarar buɗe manyan ayyukan raya jiha da Gwamna Nyesom Wike ya gayyaci Zaɓaɓɓen Shugaban Ƙasa, Bola Tinubu.
Tinubu ya amsa gayyatar ziyarar kwanaki biyu a Ribas domin ya ƙaddamar da gadar sama da gine-ginen kotu waɗanda Gwamna Nyesom Wike ya yi.
Tuni dai Wike ya bayyana cewa yau Laraba ranar hutu ce, kuma ya yi kira ga jama’a a fito a yi tururuwar tarbar Tinubu
Cikin wata sanarwa da Kakakin Yaɗa Labaran APC na Jihar Ribas, Darlington Nwauju ya fitar, ya ce babu ruwan su da ziyarar da Tinubu zai kai Ribas, ta ƙashin kan sa ce. Ya ce APC ta nesanta kan ta da ziyarar.
“Mu na ƙalubalantar gwamna mai barin gado Wike ya daina yi mana shisshigin tsarma mana siyasar raba kawuna. Domin babu abin da ya ke yi a Ribas sai raba kawunan ‘yan APC.
“Mu na sane yadda Wike ke ta nuna wa duniya cewa kamar APC ta mutu a Jihar Rivers, duk kuwa da ya sha furtawa a cikin hirarrakin da aka yi da shi a baya cewa, ba zai taɓa yin wata mu’amala da APC ba, domin jam’iyya ce mai ɗauke da cutar kansa.
Idan ba a manta ba, lokacin yaƙin neman zaɓe, sai da Tinubu ya kai wa Wike ziyara a Gidan Gwamnatin Jihar Ribas.
A wurin ne har Wike ya shawarci Tinubu, ya ce masa kada ma ya yi asarar kuɗaɗen sa a zaɓen gwamna, domin ɗan takarar APC dai na jihar ba zai iya taɓuka komai ba.