Wasu mazaunan babban Birnin Tarayya Abuja sun koka da yadda ba a samun sabbin takardun kudade domin gudanar harkokin yau da kullum.
Idan ba a babban bankin Najeriya CBN ya amince a ci gaba da amfani da tsoffin takardun kudi na naira 200, 500 da 1,000 daga nan har zuwa ranar 31 ga Disemba 2023.
Wani wakilin Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya NAN da ya zazzagaya cikin Abuja ya bayyana yadda mutane ke kokawa da rashin sabbin takardun kudaden.
Wani mazaunin Nyanya Moses Nnegedu ya ce idan har CBN da gaske ya ke dole ayi amfani da sabbin kudaden, kamata yayi ya tilasta bankunan kasuwanci su rika sakin kudaden ga mutane.
“ Na yi amfani da sabon kudi makonni biyu da suka wuce amma tun daga wannan rana ban sake samun kudin ba saboda karancin su da ake fama dashi.
Wani Mazaunin Garki Gabriel Daniel ya ce baya tsamanin wa’adin da gwamnati ta bada na ranar 31 ga Disamba domin daina amfani da tsoffin takardun kudade zai yiwu a kasar nan.
“Na manta ranar da na kashe sabbin kudi domin ko a cikin banki da ATM tsoffin takardun kudi suke biyan mutane da su.
Daniel ya ce babban matsalar da muke fama da shi a kasar nan shine yadda babu gwamnatin da ta ke maida hankali wajen zantar da kudirorin da take tsarawa.
“Tun lokacin da gwamnati ta sanar cewa a rika karbar tsoffin takardun kudi sabbin da ake gani suka bace.
Abbah Moses mazaunin Gwagwalada ya ce masu kudin kasar nan sun karbe sabbin kudaden suna Kuma boye da su sai bayan ranar 31 ga Disamba za su fito da su.
“A dalilin haka ya sa ko da kananan bankuna sun saki sabbin kudaden wasu tunda suna boyewa ba zai Isa kowa ya samu a kasar ba.
“Idan ba a yi hankali ba wahalan da mutane suka sha a wancan lokacin na rashin kudi zai fi tsananta ana ganin Disambar da nisa ne.
Discussion about this post