• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    2015-2023: ‘Na yi sukuwa ta lafiya, na kai zamiya lafiya’ – Buhari

    BANKWANA DA BUHARI: ‘Tinubu yau mafarkin ka ya zama gaskiya, Allah ya sa ka kai Najeriya fiye da inda na kai ta’ – Nasihar Buhari ga Asiwaju

    Tsakanin Sanata Barau da Gwamna Ganduje, Daga Jaafar Jaafar

    Ba zan jira Litinin ba, tun Lahadi zan mika mulki ga Abba Gida-Gida in kama gaba na – Ganduje

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    An Karrama gidan Jaridar PREMIUM TIMES da kyauta mafi daukaka a aikin Jarida na kasar Amurka

    BA DA MU BA, TAYA ƁERA ƁARI: PREMIUM TIMES ta nesanta kan ta daga ƙungiyar da ta jona sunan ta a shirya taron karrama wasu mutane

    KIRAN RUWA: ‘Ka wa Allah ka ɗaga mana kafa, kada ka kwace mana filayen mu har 9 da ka kunno kai a kan su – Makarfi ga El-Rufai

    KIRAN RUWA: ‘Ka wa Allah ka ɗaga mana kafa, kada ka kwace mana filayen mu har 9 da ka kunno kai a kan su – Makarfi ga El-Rufai

    ‘Ni da Wike kaman ‘Yan biyu ne, muna tsage gaskiya komai dacin ta’ – El-Rufai

    ‘Ni da Wike kaman ‘Yan biyu ne, muna tsage gaskiya komai dacin ta’ – El-Rufai

    SABODA TIWITA: Sanatocin PDP sun fice daga Zauren Majalisar Dattawa

    Zaɓaɓɓun Sanatocin Arewa ta Tsakiya sun nemi a ba su Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Ko a-yi-ta-ta-ƙare

    KIDAYA: An kashe naira biliyan 200 wurin shirye-shiryen fara ƙidayar jama’a – Shugaban Ƙidaya

    KIDAYA: An kashe naira biliyan 200 wurin shirye-shiryen fara ƙidayar jama’a – Shugaban Ƙidaya

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    2015-2023: ‘Na yi sukuwa ta lafiya, na kai zamiya lafiya’ – Buhari

    BANKWANA DA BUHARI: ‘Tinubu yau mafarkin ka ya zama gaskiya, Allah ya sa ka kai Najeriya fiye da inda na kai ta’ – Nasihar Buhari ga Asiwaju

    Tsakanin Sanata Barau da Gwamna Ganduje, Daga Jaafar Jaafar

    Ba zan jira Litinin ba, tun Lahadi zan mika mulki ga Abba Gida-Gida in kama gaba na – Ganduje

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    An Karrama gidan Jaridar PREMIUM TIMES da kyauta mafi daukaka a aikin Jarida na kasar Amurka

    BA DA MU BA, TAYA ƁERA ƁARI: PREMIUM TIMES ta nesanta kan ta daga ƙungiyar da ta jona sunan ta a shirya taron karrama wasu mutane

    KIRAN RUWA: ‘Ka wa Allah ka ɗaga mana kafa, kada ka kwace mana filayen mu har 9 da ka kunno kai a kan su – Makarfi ga El-Rufai

    KIRAN RUWA: ‘Ka wa Allah ka ɗaga mana kafa, kada ka kwace mana filayen mu har 9 da ka kunno kai a kan su – Makarfi ga El-Rufai

    ‘Ni da Wike kaman ‘Yan biyu ne, muna tsage gaskiya komai dacin ta’ – El-Rufai

    ‘Ni da Wike kaman ‘Yan biyu ne, muna tsage gaskiya komai dacin ta’ – El-Rufai

    SABODA TIWITA: Sanatocin PDP sun fice daga Zauren Majalisar Dattawa

    Zaɓaɓɓun Sanatocin Arewa ta Tsakiya sun nemi a ba su Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Ko a-yi-ta-ta-ƙare

    KIDAYA: An kashe naira biliyan 200 wurin shirye-shiryen fara ƙidayar jama’a – Shugaban Ƙidaya

    KIDAYA: An kashe naira biliyan 200 wurin shirye-shiryen fara ƙidayar jama’a – Shugaban Ƙidaya

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

Yadda Gogarma Dogo Giɗe ya sako ɗaliban Kwalejin Yauri 4, bayan karɓar fansar naira miliyan 80

Ashafa MurnaibyAshafa Murnai
April 23, 2023
in Labarai
0
AREWA A HANNUN ‘YAN BINDIGA: Tattaki a Daular Dogo Giɗe da Ali Kachalla, riƙaƙƙun ‘yan ta’addar da ke yadda suka ga dama a Arewa,suka gagari gwamnati

Daga cikin sauran ɗalibai mata 11 da ke hannun gogarman ɗan bindiga Dogo Giɗe, wanda ya sace ɗalibai sama 100 a cikin 2021, cikin wannan makon an sako 4, yanzu saura 7 kenan a hannun tantirin ɗan bindigar.

Dogo Giɗe ya sako ɗaliban mata su 4 bayan an biya kuɗin fansa har naira miliyan 80, tare da shafe kwanaki shida ana tattauna yadda za a sako su tsakanin ɗan bindigar da iyayen yaran.

Ɗalibai huɗun da aka sako su ne Bilha Musa, Faiza Ahmed, Rahma Abdullahi da Hafsa Murtala.

PREMIUM TIMES ta ji daga bakin ɗaya daga cikin iyayen yaran da aka sako ɗin cewa Dogo Giɗe ya sake su bayan an biya shi fansar naira miliyan 80.

Ya ce an sake su a ranar Juma’a, ƙarfe 8:37, kamar yadda wanda ya ke shugaban ƙungiyar iyayen ɗaliban da aka yi garkuwa da su a Kwalejin Tarayya ta Yauri ya shaida wa wakilin mu.

Ɗaliban mata su huɗu dai ko da aka bayar da su, sai Giɗe ya sa yaran sa uku su ka ɗauke su kan babura, su ka kai su wani ƙauye wajen Ƙaramar Hukumar Koko a Jihar Kebbi. Daga can ne kuma masu jiran su karɓi yaran su ka karɓe su zuwa Birnin Kebbi, babban birnin Jihar Kebbi.

Giɗe da yaran sa sun yi garkuwa da ɗaliban cikin Yuni, 2021 a Kwalejin Gwamnatin Tarayya ta Yauri a Jihar Kebbi, inda su ka kwashi ɗalibai sama da 100.

Daga baya sun riƙa sako su, amma a ƙarshe su ka riƙe mata 11. Da yawa an sako su bayan an riƙa biyan diyya, wasu kuma an sako su bayan gwamnati ta saki wasu yaran Dogo Giɗe da aka kama.

Ɗaya daga cikin iyayen ɗaliban mai suna Sani Mohammed, ya shaida wa wakilin mu cewa an biya fansar naira miliyan 80 kafin Dogo Giɗe ya saki ɗaliban 4.

Ya ce Giɗe ne da kan sa ya zaɓi waɗanda zai saki daga cikin matan 11 da ke hannun sa. Yanzu bakwai kenan su ka rage ba a kai ga saki ba.

“A maganar ƙarshe da mu ka yi da shi, ya yi alƙawarin idan aka cika masa kuɗin da ya ke nema a biya shi, to zai saki sauran.

“Har yanzu bai saki ɗiya ta ba. Amma dai mu na sa rai cewa nan ba da daɗewa ba zai sake ta,” inji Sani.

Sani wanda tsohon ma’aikacin gwamnati ne da ya yi ritaya, ya shaida wa wakilin mu cewa sun shafe kwanaki shida su na tattaunawa da ‘yan bindiga kafin su amince su saurare su.

“Ka san da farko cewa ya yi naira miliyan 100 ya ke so a biya shi. To dai wata rana sai ya kira ni, na shaida masa gaskiyar halin da ake ciki na tsananin rayuwa. Sai ya ce zai iya rage naira miliyan 20. Don haka a biya naira miliyan 80 kenan,” inji Sani.

Wakilin mu ya ji cewa wani Abubakar mai shiga tsakanin iyayen da kuma su Dogo Giɗe. Iyayen da kuma Dogo Giɗe duk sun amince da gaskiyar Abubakar. Kafin Abubakar dai sau uku ana canja mai shiga tsakani, saboda rashin amincewa a tsakanin su.

Salim Kaoje wanda shi ne shugaban iyayen yaran da ke hannun su Giɗe, ya tabbatar wa wakilin mu cewa mai shiga tsakanin da wasu iyayen yaran su biyu su na cikin daji, su na roƙon Giɗe ya taimaka ya saki sauran yaran bakwai da ke hannun sa.

“Waɗanda Ya saki su huɗu mu ne mu ka sayar da kadarorin mu, mu ka haɗa kuɗaɗen, sai kuma gudummawar da jama’ar da ke tausaya mana su ka riƙa bayarwa. Amma babu ko sisi na gwamnati,” inji shi.

Kaoje ya ce har yanzu akwai ƙanuwar sa Farida a hannun Giɗe, a cikin waɗanda ba a sako ba.

Ya ce an yi tsammanin gaba ɗaya Giɗe zai saki, amma sai ya saki huɗu ya riƙe bakwai. “Wannan shi ne dalilin da ya sa mai shiga tsakani da iyayen biyu har yanzu su ke cikin daji, su na roƙon sa ya saki sauran ɗalibai bakwai da ke hannun sa.”

Labari Mai Ban-takaici: Yadda Gogarma Dogo Giɗe Ya ‘Auri’ ‘Ya Ta Farida Wacce Ya Kama A Kwalejin Yauri, Cikin 2021 -Sani Yauri, Mahaifin Farida:

Masu karatu su fahimci cewa PREMIUM TIMES Hausa ta buga wannan labari mai ban-tausayi da takaici tun cikin watan Satumba, 2022:

Cikin wata tattaunawa da mai ban-tausayi, cike da damuwa ƙuncin rayuwa, Sani Giɗe ya shaida wa wakilin mu yadda a halin ‘yanzu ‘yar sa Farida Sani ke hannun gogarman ‘yan bindiga Dogo Giɗe, a matsayin amaryar sa da ya yi wa auren-dole, bayan sun kai hari a Kwalejin Gwamnatin Tarayya ta Yauri, ranar 17 Ga Yuni, 2021.

Idan ba a manta ba, a farmakin dai an kwashi ɗalibai 90 da kuma malamai. Amma an riƙa ceto wasu, daga baya kuma an riƙa tattaunawa da Gwamnatin Jihar Kebbi ana sakin wasu da kaɗan-kaɗan.

Zuwa cikin watan Janairu lokacin da aka saki ƙarin ɗalibai 30, saura ‘yan mata 11 ne su ka rage wurin su Dogo Giɗe, waɗanda ya tabbatar da cewa sun raba su a tsakanin su ‘yan bindigar, sun aurad da su, saboda Gwamnati ta ƙi biyan su kuɗin fansar da su ka nemi a biya su.

Sani Kaoje shi ne mahaifin ɗaya daga cikin ɗalibai mata da su Gogarma Dogo Giɗe su ka aura. Ya shaida wa PREMIUM TIMES irin yadda ya riƙa waya da Dogo Giɗe sau tarin yawa dangane da ‘yar sa da har yanzu ke hannun sa, a matsayin amaryar sa.

“Ina da ‘ya’ya 19 kuma mata na uku. Farida ita ce ta 15, kuma yanzu shekarun ta 16. Wato kenan ta na da shekaru 15 aka yi garkuwa da ita” Inji Sani Kaoje.

Ya shaida cewa sau da yawa Dogo Giɗe na kiran sa ya na nuna masa cewa tun da ba za a biya su naira miliyan da babura 30 da su ka nema ba, to za su auri yaran.

“Na sha yin waya da shi. Saboda ya na kira na sosai. Har dai ta kai ya nuna min cewa sun auri yaran. Bai fito ya nuna min cewa shi ya auri Farida ‘ya ta mai shekaru 15 a lokacin da aka kama ta ba. Amma sai ya karkatar da maganar ya ce min ta na hannun sa, shi ke kula da ita. Amma daga ƙarshe ya ce min matar sa ce, kuma ko ya mutu, a cikin gidan su akwai wanda zai gaje ta.”

Kaoje ya ce tabbas ya na yin waya da ‘yar sa Farida ba sau ɗaya ko sau biyu ba. Amma dai Dogo Giɗe ɗin ne ke kiran sa a waya, sai ya haɗa su su gaisa.

“Akwai ranar da ya haɗa da ita mu ka yi waya, ta kira ni ta ce min Baba akwai fa matsala, saboda za su aurad da mu.” Ni kuma dama ya rigaya ya shaida min haka.

Sani Yauri ya nuna gazawar Ministan Harkokin Ilmi Adamu Adamu, wanda ya ce bai yi komai ba, duk kuwa da cewa makarantar da aka sace yaran ta Gwamnatin Tarayya ce.

Sannan kuma ya shaida wa wakilin mu cewa Dogo Giɗe ya ce shi Gwamnati ya ke so ta sasanta da su, ba iyayen yaran ba.

“Dogo Giɗe ya ce min tun su na neman a biya su fansar naira miliyan 100, su ka rage su ka ce a biya naira miliyan 50 da babura 30, amma gwamnati ta yi banza da su. Wai shi ya sa su ka yanke shawarar aurar da sauran ‘yan matan da su ka rage a hannun su.” Inji Sani Yauri, wanda tsohon ma’aikacin gwamnati ne daya yi ritaya.

A ƙarshe ya nuna irin halin ƙuncin da su ke ciki, tun daga ranar da aka yi garkuwa da ‘ya’yan su har yau ɗin nan.

“Wasu iyayen sun mutu saboda takaici. Akwai kuma mahaifin wata ƙawar ‘ya ta mai suna Rebecca. To mahaifin ta ya shiga damuwar da ba ya iya hasala komai a rayuwa. Ko kuɗi ka miƙa masa, ba zai iya ƙidaya su ba.”

Tags: DOgoKebbiKuɗiLabaraiNews
Previous Post

SIYAN KURI’A DALA MILIYAN 1: ‘Ƙarya gwamnoni su ke yi

Next Post

BUKIN SALLAH: El-Rufai, Uba Sani sun yaba da hawan Sarkin ‘Kara’ na masarautar Lere

Ashafa Murnai

Ashafa Murnai

Next Post
BUKIN SALLAH: El-Rufai, Uba Sani sun yaba da hawan Sarkin ‘Kara’ na masarautar Lere

BUKIN SALLAH: El-Rufai, Uba Sani sun yaba da hawan Sarkin 'Kara' na masarautar Lere

Discussion about this post

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • BANKWANA DA BUHARI: ‘Tinubu yau mafarkin ka ya zama gaskiya, Allah ya sa ka kai Najeriya fiye da inda na kai ta’ – Nasihar Buhari ga Asiwaju
  • Kotu ta tsige Kori Sufeto Janar din ‘yan sandan Najeriya Usman Baba, ta ce zaman sa IG ya haramta bisa doka
  • Diezani ta maka EFCC da Ministan Shari’a kotu, ta na neman diyyar naira biliyan 100, saboda sun kira ta ‘ɓarauniya’
  • Ba zan jira Litinin ba, tun Lahadi zan mika mulki ga Abba Gida-Gida in kama gaba na – Ganduje
  • JAWABIN BANKWANA: Na gama da ku lafiya, inda na gaza kuma a yayyafe – Buhari

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.