Tsohon ɗan takarar jam’iyyar HDP a zaɓen shugaban ƙasa, Ambrose Owuru, ya nemi Kotun Ɗaukaka Ƙara kada ta bari a rantsar da Bola Tinubu matsayin shugaban ƙasa a ranar 29 Ga Mayu.
Wannan ƙara da Ambrose na HDP ya shigar, ita ce ƙara ta shida da jam’iyyu da ‘yan takara daban-daban su ka shigar su na nuna rashin amincewa da nasarar Bola Tinubu na APC.
Sai dai su waɗancan biyar ɗin, sun maka Bola Tinubu ƙara ce a Kotun Ɗaukaka Ƙararrakin Zaɓen Shugaban Ƙasa, shi kuwa Ambrose a Kotun Ɗaukaka Ƙara ya kai ta sa ƙarar.
Daga cikin waɗanda su ka maka Tinubu ƙara kotu, akwai PDP da Atiku Abubakar, LP da Peter Obi.
A ƙara mai lamba CA/CV/259/2023 wadda Ambrose ya shigar, ya nemi a dakatar da rantsar da Bola Tinubu. Kuma a cikin waɗanda ya ke ƙara, ya haɗa har da Shugaba Muhammadu Buhari da Antoni Janar Abubakar Malami da kuma Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC).
Ambrose Owuru wanda lauya ne, ya yi takara tun a zaɓen 2019 a ƙarƙashin HDP, kuma ya sha kaye a hannun Buhari, amma sai ya yi iƙirarin cewa shi ne ya yi nasara.
A kan haka ne Ambrose Owuru ya haƙiƙice cewa shi ne ya yi nasara, amma aka ba Buhari.
Don haka ya ce wa kotu Tinubu ba zai yiwu ya zama shugaban ƙasa ba a 2023, har sai an rantsar da shi Ambrose ɗin ya yi shekaru huɗu na zangon sa tukunna.
Hujjar Da Ambrose Owuru Ke Taƙama Da Ita:
Ya ce, “Shugabancin Muhammadu Buhari na 2019 zuwa 2023 haramtacce ne, domin an rantsar da shi alhali Kotun Ƙoli ba ta yanke hukuncin ƙarar Buhari da ya shigar kan zaɓen Buhari ba.
Saboda haka ya nemi kotu ta hana “miƙa mulki daga hannun Buhari zuwa hannun Bola Tinubu a ranar 29 Ga Mayu. Sannan kuma ta hana rantsar da Tinubu ɗin, saboda Kotun Ƙoli ba ya yanke hukuncin ƙarar zaɓen Buhari da ya kai tun cikin 2019 ba.”
Lauyan Ambrose Owuru mai suna Odion Peter, ya roƙi Kotun Ɗaukaka Ƙara ta gaggauta yanke hukuncin ƙarar da ya shigar kafin ranar rantsarwa.
Discussion about this post