Masu garkuwa sun gudu da tsohon Shugaban Ƙungiyar Lauyoyi ta Ƙasa, Okey Wali daga gidan sa.
An arce da shi da ƙarfin tsiya daga gidan sa, a safiyar Litinin.
Ƙungiyar Lauyoyi ta Ƙasa ce ta bayar da sanarwar tabbacin kama yin garkuwar da shi a ranar Talata.
Okey dai babban lauya ne, wato SAN, kuma an kama shi kan hanyar Obio/Akpor cikin Jihar Ribas.
Shugaban Ƙungiyar Lauyoyi ta Ƙasa na yanzu, Yakubu Maikyau ya roƙi Sufeto Janar na ‘Yan Sanda Alƙali Usman da Kwamishinan ‘Yan Sandan Jihar Ribas su yi iyakar ƙoƙarin tabbatar da ceto tsohon shugaban lauyoyin na Najeriya.
Wali Okey ya yi shugabancin NBA tsakanin 2012 zuwa 2014.
Sanarwar ta ce Wali Okey ya Yi wa ƙungiyar lauyoyi aiki tuƙuru a zamanin da ya yi shugabancin NBA.
Discussion about this post