Cikin makon jiya ne aka nuno Gwamna Abdullahi Ganduje na Kano ya na neman afuwar dukkan waɗanda ya yi wa ba daidai ba a shekaru takwas da ya yi ya na mulki.
A bidiyon, Ganduje ya yi kalamai a cikin murya mai taushi, inda ya bayyana cewa shi dai ya yafe wa kowa. Don haka ya na roƙon shi ma duk wanda ya yi wa ba daidai ba, to ya yafe masa.
Sai dai kuma Buhari da Ganduje sun sha martani daga ‘yan Najeriya, musamman talakawa, kuma matasa ‘yan soshiyal midiya.
Da yawa sun nuna yafiya da alhinin rabuwa da su biyu ɗin kan mulki. To sai dai kuma da dama sun riƙa tunatar da su irin halin ƙuncin da su ka jefa jama’a a ciki.
Da dama sun riƙa tuna wa Buhari irin masifar tsadar rayuwa da ake ciki, inda farashin kayayyaki ya nunka kuma ya sake ruɓanyawa, maimakon a ce an samu sauƙi, domin an zaɓi Buhari ne don a samu sauƙin.
Wasu kuma sun riƙa magana kan ɗimbin mutanen da ‘yan bindiga su ka kashe, su ka talauta da kuma waɗanda a yanzu haka ke tsare a hannun ‘yan bindiga.
Yayin da Buhari zai sauka daga mulki a ƙarshen watan Mayu, tuni Gwamantin Tarayya ta fara shirye-shiryen cike tallafin fetur, wanda hakan ke nuna farashin lita zai doshi Naira 500 kenan.
Buhari wanda ya hau mulki Dalar Amurka ba ta kai Naira 300 a kasuwar ‘yan canji ba, zai sauka ya bar ta wajen Naira 750.
Ya hau mulki ana kukan kuɗin aikin Hajji na naira 850,000, amma zai sauka a daidai lokacin da za a biya Naira miliyan 3 ba ‘yan canji.
Shi ma Ganduje ya sha jinjina kuma ya sha kwankwatsa a soshiyal midiya. An riƙa danganta lamarin gwamnan da rawar da ya taka a siyasa, lamurra na addini, raba filaye da sauran zarge-zargen da aka yi masa a baya.
Discussion about this post