• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TSAUTSAYI: Yadda ‘yan bindiga suka ware da Lami Awarware da Haulatu bayan halartar taron rantsar da Uba Sani a Kaduna

    Sojojin Najariya sun kara ragargaza wa Boko Haram motocin yaki bakwai

    Sojoji sun dagargaza matatun mai 47 sun kama barayin mai 65 – Hedikwatar tsaro na kasa

    HAJJI 2023: Yadda jirgin maniyyatan Jigawa ya koma Kano ba shiri, bayan ya samu matsala cikin sararin samaniyar Kamaru

    HAJJI 2023: Yadda jirgin maniyyatan Jigawa ya koma Kano ba shiri, bayan ya samu matsala cikin sararin samaniyar Kamaru

    GANAWAR TINUBU DA NLC: Ƙungiyar Ƙwadago ta ce a tilas a soke ƙarin kuɗin mai, an shammaci ‘yan Najeriya

    GANAWAR TINUBU DA NLC: Ƙungiyar Ƙwadago ta ce a tilas a soke ƙarin kuɗin mai, an shammaci ‘yan Najeriya

    Buhari-signing-2020-budget

    Gwamnatin tsohon shugaban kasa Buhari ta sanar da sabbin nade-nade a daidai ana rantsar da Tinubu shugaban kasa

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    2015-2023: ‘Na yi sukuwa ta lafiya, na kai zamiya lafiya’ – Buhari

    BANKWANA DA BUHARI: ‘Tinubu yau mafarkin ka ya zama gaskiya, Allah ya sa ka kai Najeriya fiye da inda na kai ta’ – Nasihar Buhari ga Asiwaju

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TSAUTSAYI: Yadda ‘yan bindiga suka ware da Lami Awarware da Haulatu bayan halartar taron rantsar da Uba Sani a Kaduna

    Sojojin Najariya sun kara ragargaza wa Boko Haram motocin yaki bakwai

    Sojoji sun dagargaza matatun mai 47 sun kama barayin mai 65 – Hedikwatar tsaro na kasa

    HAJJI 2023: Yadda jirgin maniyyatan Jigawa ya koma Kano ba shiri, bayan ya samu matsala cikin sararin samaniyar Kamaru

    HAJJI 2023: Yadda jirgin maniyyatan Jigawa ya koma Kano ba shiri, bayan ya samu matsala cikin sararin samaniyar Kamaru

    GANAWAR TINUBU DA NLC: Ƙungiyar Ƙwadago ta ce a tilas a soke ƙarin kuɗin mai, an shammaci ‘yan Najeriya

    GANAWAR TINUBU DA NLC: Ƙungiyar Ƙwadago ta ce a tilas a soke ƙarin kuɗin mai, an shammaci ‘yan Najeriya

    Buhari-signing-2020-budget

    Gwamnatin tsohon shugaban kasa Buhari ta sanar da sabbin nade-nade a daidai ana rantsar da Tinubu shugaban kasa

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    2015-2023: ‘Na yi sukuwa ta lafiya, na kai zamiya lafiya’ – Buhari

    BANKWANA DA BUHARI: ‘Tinubu yau mafarkin ka ya zama gaskiya, Allah ya sa ka kai Najeriya fiye da inda na kai ta’ – Nasihar Buhari ga Asiwaju

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

Manya-manyan Ƙalubalen Da Ke Gaban Zaɓabben Gwamnan Zamfara, Dauda Lawal

Ashafa MurnaibyAshafa Murnai
April 25, 2023
in Babban Labari
0
Manya-manyan Ƙalubalen Da Ke Gaban Zaɓabben Gwamnan Zamfara, Dauda Lawal

A yanayin ƙaramar jiha mai ƙananan hukimomi 14 kamar Zamfara, wacce ba ta da wata hanyar samun kuɗin shiga sai zaman tsammanin jiran kason kuɗaɗen Gwamnatin Tarayya, masu sharhi na ganin cewa naɗa kwamishinoni har 26 a ma’aikatu 26, almubazzaranci ne kawai.

A zaɓen gwamnonin 2023, babu ɗan takarar da aka yi wa taron dangin gaggan tsoffin turaye, tsoffin kuraye da guma-guman tsoffin ‘yan alewa, kamar irin yadda aka yi wa zaɓaɓɓen gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal na PDP.

Dauda Lawan ya yi damben da ba a taɓa ganin sabon-yanka-raken ɗan siyasa ya yi irin sa kuma ya yi nasara ba.

Dauda ya buge ‘Shagon Maradun’, Gwamna Bello Matawalle. Kuma ya buge ‘Shagon Bakura’, Sanata Ahmed Sani Yarima. Sannan ya tattake ‘Shagon Mafara’, Abdul’aziz Yari, kuma ya buge ‘Shagon Shinkafi’, Mamuda Aliyu, waɗanda su huɗun su ka yi masa taron dangi, amma duk sai da ya yi masu kakkaɓar-‘ya’yan-kaɗanya.’

A ce ka na sabon ɗan siyasa, amma ka kayar da gungun tsoffin gwamnoni uku tare da Gwamna da ke kan mulki, zai yi wuya a ce akwai bajintar da ta fi wannan a siyasa.

Sauran waɗanda su ka yi masa taron-dangi har da sanatoci da mambonin tarayya da ke kan kujera, kai da duk wani gadagurun wane da wane ko wane ɗan wanen Zamfara.

Sai dai kuma wannan nasara da ya samu, za a iya cewa murnar ta ɗan taƙaitaccen lokaci ne, idan aka yi la’akari da irin manya-manyan ƙalubalen da ke gaban Gwamna Mai Jiran Gado, Dauda Lawal. Daga ranar da za a rantsar da shi a 29 ga Mayu, 2023, to daga ranar ce zai gane cewa lallai ya ɗauko Dala ba gammo.

Dauda Lawal Da Ƙalubalen Talauci Da Yunwa A Zamfara:

Hukumar Ƙididdigat Alƙaluman Bayanai ta Ƙasa (NBS), wadda mallakar Gwamnatin Tarayya ce, ta ce kashi 78 bisa 100 na al’ummar jihar duk matalauta ne. Noman da jihar ke tutiya da shi, yanzu tuni ya samu cikas, sakamakon ‘yan bindigar da su ka ragargaje Zamfara.

Rahoton 2021 da IFRC ta fitar ya ce mutum milyan 2.53 ne daga Arewa maso Yamma ciki har da Zamfara, Katsina da Sakkwato da Katsina, duk za su fuskanci tsananin yunwa da ƙarancin abinci, sadadiyyar hare-haren ‘yan bindiga.

BudgiT ta fitar n Zamfara ce ta 32 a jerin sunayen jihohin da ke fama da talauci, tantagaryar sa.

Kashi 80 bisa 100 na al’ummar Zamfara manoma ne. Amma saboda tsananin bala’in hare-haren ‘yan ta’adda ya sa manoma da sauran talakawa an gudu daga yankunan karkara.

Daga 2019 zuwa 2021 rahoto ya ce Zamfara ba ta tsinana wani abin tasiri ga tattalin arzikin jihar ba.

Kasancewar sa ƙwararren ma’aikacin banki, ana kyautata wa Dauda Lawal zaton zai gaggaci masu zuba jari zuwa Zamfara, wanda yin hakan zai samar wa ɗimbin matasa masu zauna-gari-banza za su samu aikin yi.

Wata matsala ita ce matsalar rashin ingantattun kasuwanni. Idan ka cire Babbar Kasuwa Gusau, to dukkan sauran su na buƙatar a inganta su, ko ma a sake gina su baki ɗaya.

Dauda Lawal Da Ƙalubalen Matsalar Tsaro:

Wani rahoton da jihar ta fitar ya ce tsakanin 2011 zuwa 2019, an yi garkuwa mutum 3,672, sannan an biya kuɗin fansa har Naira biliyan 3. An bar mata da ƙananan yara 4,983, waɗanda aka kashe mazajen su ko iyayen su. An maida ƙananan yara 25,050 marayu. Mutum 190,340 sun rasa gidajen su.

Lamari ya ƙara lalacewa, ta yadda yanzu mahara su na kai hari cikin manyan garuruwan Zamfara, irin su Gusau, Kaura Namoda da Talata Mafara.

Ya zama wajibi gwamna mai jiran gado idan ya hau, ya bijiro da hanyoyin kawo ƙarshen rikicin jihar Zamfara, wanda tilas ya samar da fahimtar juna tsakanin Fulani makiyaya da Hausawa musamman a yankunan karkara.

Sannan akwai buƙatar inganta ilmi, kiwon lafiya da sauran su. Kasancewar a jihar Zamfara ce aka fi samun mutuwar jirajirai a ƙasar nan, kamar yadda rahoto ya tabbatar a cikin 2020. A cikin jarirai 100,000, aƙalla 576 ke mutuwa a Zamfara. A ƙasar nan kuwa aƙalla 197 ke mutuwa a cikin 100,000.

Dauda Lawal zai fuskanci ƙalubalen matsalar likitoci da ƙarancin asibitoci.

Matsalar ilmi kuwa ita ma zaune ta ke da gindin ta a Zamfara.UNESCO ta ce akwai yara masu gararamba ba su zuwa makaranta har 883,952.

Matsalar bashi ma gagarimar abu ce a Zamfara. DMO ta ce zuwa Disamba 2022, ana bin Gwamnatin Zamfara bashin Naira 112,197,059,996. Wannan fa bashin cikin gida ne kaɗai. Na waje kuwa ana bin Najeriya bashin N28,861,053.

“Cikin 2022, kashi 45.9 na kuɗaɗen da Zamfara ta kashe, duk a biyan bashi su ka tafi. Sauran kashi 54.1 kuma wajen biyan albashi, kuɗaɗen ‘yan fansho, tafiyar da ofisoshi da wasu ‘yan ayyukan raya ƙasa da ba a rasa ba. Wannan kuma babbar kasada ce,” inji Mohammed.

A matsalar ilmi, Hukumar Jarabawar NECO na bin Jihar Zamfara bashin naira biliyan 1.3. na NECO da WAEC. Akwai buƙatar Lawal ya iya biyan kuɗaɗen, domin a fito wa ɗaliban da sakamakon su.

Saboda a 2022 Jihar Zamfara ba ta yaye ɗalibin sakandare ko ɗaya a jarabawar WASSCE, saboda ba a biya masu kuɗin jarabawar ba.

Ma’aikata sun yi wa jihar yawa. Jiha mai ƙananan hukumomi 14, amma kwamishinoni da ma’aikatu har 26. Sannan babu wata hanyar samun kuɗaɗen shiga, sai an jira kuɗaɗen kason Gwamnantin Tarayya, wannan ganganci ne da almubazzaranci.

Tags: DaudaNajeriyaPREMIUM TIMES
Previous Post

Masu lambobin waya a Najeriya sun kai mutum miliyan 222.5 – NBS

Next Post

Nan da kwanaki biyar yawan mutanen Indiya zai zarce yawan mutanen Chana

Ashafa Murnai

Ashafa Murnai

Next Post
Nan da kwanaki biyar yawan mutanen Indiya zai zarce yawan mutanen Chana

Nan da kwanaki biyar yawan mutanen Indiya zai zarce yawan mutanen Chana

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • Yadda bashin Dala Miliyan 95 na Bankin Musulunci ya bunƙasa noma a ƙananan hukumomin Kano 44 – Hamisu, Kodinetan KSADP
  • Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati
  • Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki
  • TSAUTSAYI: Yadda ‘yan bindiga suka ware da Lami Awarware da Haulatu bayan halartar taron rantsar da Uba Sani a Kaduna
  • Gwamnatin Kano ta hana lika fastoci a ginegine a fadin jihar

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.