An yi garkuwa da ɗan takarar mataimakin gwamnan Jihar Cross River na jam’iyyar YPP, Agbor Onyi.
Tuni dai Rundunar ‘Yan Sandan Jihar ta Cross River su ka tabbatar cewa an yi garkuwa da shi ne da wasu mutum uku, waɗanda cikin su har da Mataimakin Sufurtandan Imagireshin.
Kakakin Yaɗa Labaran ‘Yan Sanda na jihar, Irene Ugbo ta shaida wa manema labarai cewa an sace su a ranar Alhamis, kan hanyar Kalaba zuwa Ogoja.
Ta bayyana sunan jami’in Imagireshin da Imojara Imojara.
Ta ce an yi garkuwa da su huɗun ne yayin da su ke kan hanyar tafiya garin su domin yin zaɓe.
“Waɗanda tsautsayin ya ritsa da su, su na kan hanyar tafiya ce a cikin motar ƙirar Toyota Corolla, lokacin da masu garkuwa su ka tare su, kuma su ka yi cikin daji da su.
“Ɗaya daga cikin waɗanda ke cikin motar matar wani hadimin Gwamna Ben Ayade ce”. Inji Kakakin ‘Yan Sanda.
Yan sanda sun ce su na bakin ƙoƙarin gano su kuma su ceto su.
Majiya ta bayyana cewa masu garkuwa sun nemi a biya su Naira miliyan 60, amma daga baya su ka rage zuwa Naira miliyan 40.
Tuni dai a wasu rumfunan zaɓe aka fara kaɗa ƙuri’u a jihohi daban-daban.
Discussion about this post