Shugaban Hukumar Zaɓe (INEC) ta Ƙasa, Farfesa Mahmood Yakubu ya bayyana Bola Tinubu, ɗan takarar shugaban ƙasa na APC a matsayin zaɓaɓɓen shugaban ƙasa, wanda ya yi nasarar lashe zaɓen 2023.
Tinubu ya doke sauran ‘yan takara 17, bayan ya samu ƙuri’u 8,794,726. Wato ƙuri’un sa sun fi na kowane ɗan takara yawa.
Sannan kuma ya samu kashi 25 bisa 100 a jihohi 30, fiye ma jihohi 24 da dokar zaɓe ta ce tilas sai wanda ya yi nasara ɗin ya samu.
Shugaban INEC ya bayyana sakamakon zaɓe kusan asubahin ranar Laraba, ya ce Atiku Abubakar na PDP ne ya zo na biyu da ƙuri’u 6,984,520.
Peter Obi na LP ya zo na uku da ƙuriu 6,101,503, sai Rabi’u Kwankwaso na NNPP ya zo na huɗu da ƙuri’u 1,496,687.
Yakubu ya ce za a bai wa Tinubu satifiket na lashe zaɓe ƙarfe 3 na ranar Laraba a Cibiyar Tattara Sakamakon Zaɓe.
Tinubu ya lashe Ribas, Barno, Jigawa, Zamfara, Benuwai, Kogi, Kwara, Neja, Osun, Ekiti, Ondo, Oyo da Ogun.
Atiku ya lashe Katsina, Kebbi, Sokoto, Gombe, Yobe, Bauchi, Taraba, Adamawa da Akwa Ibom, Osun da Bayelsa.
Peter Obi ya lashe Cross Riba, Delta, Legas, FCT, Filato, Imo, Ebonyi, Nasarawa, Anambra, Abiya, da Enugu.
Kwankwaso kuma ya lashe Kano kaɗai.
Discussion about this post