• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Ku fito ku ceci mutanen jihar Kaduna kamar yadda kuka yi a zaben majalisun Tarayya da na sanatoci – Isah Ashiru

    An yi mana kwange a hukuncin kotu, za mu daukaka kara – Ashiru

    SSS

    TAKE HAƘƘIN ƊAN ADAM: Yadda SSS suka riƙa faffalla min mari, suka ja ni ƙasa girrrr, don kawai na ce su bi doka – Lauya Ogbankwa

    Muna ƙarancin malamai, a janye dokar hana ɗaukar sabbin malamai da gwamnatin tarayya ta ƙaƙaba – Jami’ar ABU

    Muna ƙarancin malamai, a janye dokar hana ɗaukar sabbin malamai da gwamnatin tarayya ta ƙaƙaba – Jami’ar ABU

    TONON ASIRI: An kama wani Dagaci cikin gungun mahara a lokacin batakashi da ‘Yan sanda

    ‘Yan bindiga sun kashe mutum shida a Kaduna

    Almajirai

    UNICEF ta saka Almajirai sama da 20,000 cikin rajistar tsarin agaza wa marasa karfi a Katsina

    Majalisar Tarayya ta ce a soke ƙarin kuɗin makaranta da aka yi wa ɗaliban jami’o’i da na Kwalejojin Gwamnatin Tarayya

    KALUBALEN DA KE GABAN MAJALISAR WAKILAI TA ƘASA: Gaganiya da matsalar raɗaɗin tsadar rayuwa, matsalar tsaro da sauran su da ake fuskanta a kasa

    Yadda sojojin sama sun ragargaza sansanonin ‘yan bindiga a jihohin Katsina, Zamfara, Sokoto da Kaduna

    RASHIN TSARO: Tinubu ya amince da sayo jiragen sama masu saukar ungulu 12 ga sojojin Najeriya – Lagbaja

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    Ƴan ta’adda sun gamu da fushin sojojin Najeriya, sojoji sun kashe 50 sun kama 60

    GRAINS MARKET AT KAFIN MADAKI DISTRICT IN GANJUWA

    Yari ya raba tallafin tirela 145 cike maƙil da buhunan masara 145 ga mabuƙata a Zamfara

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    Hukumar CAF za ta binciki yadda mahaifiyar ɗan wasa ta mutu cikin 1986, shi kuma ya ce atabau cikin 1990 ta haife shi

    A karo na Uku, Moroko za ta ɗauki baƙuncin gasar cin kofin kwallon ƙafa na nahiyar Afrika a Janairun 2025

    NFF ta sake nada Chris Danjuma a matsayin kocin Falconets

    NFF ta sake nada Chris Danjuma a matsayin kocin Falconets

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    JERIN SUNAYE: Jami’o’i 51 da ba za su dauki dalibin da ya ci kasa da maki 180 a jarabawar JAMB ba

    TSARIN BAI WA ƊALIBAI RAMCE: Abubuwan da suka wajaba ɗalibai da iyaye su sani

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Ku fito ku ceci mutanen jihar Kaduna kamar yadda kuka yi a zaben majalisun Tarayya da na sanatoci – Isah Ashiru

    An yi mana kwange a hukuncin kotu, za mu daukaka kara – Ashiru

    SSS

    TAKE HAƘƘIN ƊAN ADAM: Yadda SSS suka riƙa faffalla min mari, suka ja ni ƙasa girrrr, don kawai na ce su bi doka – Lauya Ogbankwa

    Muna ƙarancin malamai, a janye dokar hana ɗaukar sabbin malamai da gwamnatin tarayya ta ƙaƙaba – Jami’ar ABU

    Muna ƙarancin malamai, a janye dokar hana ɗaukar sabbin malamai da gwamnatin tarayya ta ƙaƙaba – Jami’ar ABU

    TONON ASIRI: An kama wani Dagaci cikin gungun mahara a lokacin batakashi da ‘Yan sanda

    ‘Yan bindiga sun kashe mutum shida a Kaduna

    Almajirai

    UNICEF ta saka Almajirai sama da 20,000 cikin rajistar tsarin agaza wa marasa karfi a Katsina

    Majalisar Tarayya ta ce a soke ƙarin kuɗin makaranta da aka yi wa ɗaliban jami’o’i da na Kwalejojin Gwamnatin Tarayya

    KALUBALEN DA KE GABAN MAJALISAR WAKILAI TA ƘASA: Gaganiya da matsalar raɗaɗin tsadar rayuwa, matsalar tsaro da sauran su da ake fuskanta a kasa

    Yadda sojojin sama sun ragargaza sansanonin ‘yan bindiga a jihohin Katsina, Zamfara, Sokoto da Kaduna

    RASHIN TSARO: Tinubu ya amince da sayo jiragen sama masu saukar ungulu 12 ga sojojin Najeriya – Lagbaja

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    Ƴan ta’adda sun gamu da fushin sojojin Najeriya, sojoji sun kashe 50 sun kama 60

    GRAINS MARKET AT KAFIN MADAKI DISTRICT IN GANJUWA

    Yari ya raba tallafin tirela 145 cike maƙil da buhunan masara 145 ga mabuƙata a Zamfara

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    Hukumar CAF za ta binciki yadda mahaifiyar ɗan wasa ta mutu cikin 1986, shi kuma ya ce atabau cikin 1990 ta haife shi

    A karo na Uku, Moroko za ta ɗauki baƙuncin gasar cin kofin kwallon ƙafa na nahiyar Afrika a Janairun 2025

    NFF ta sake nada Chris Danjuma a matsayin kocin Falconets

    NFF ta sake nada Chris Danjuma a matsayin kocin Falconets

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    JERIN SUNAYE: Jami’o’i 51 da ba za su dauki dalibin da ya ci kasa da maki 180 a jarabawar JAMB ba

    TSARIN BAI WA ƊALIBAI RAMCE: Abubuwan da suka wajaba ɗalibai da iyaye su sani

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

Kwankwaso, Kwankwasiyya Da Yankan Kunkurun Bamaguje A 2023, Daga Mamman Ɗan Mamman

Premium Times HausabyPremium Times Hausa
March 10, 2023
in Ra'ayi
0
2023: Ko matasa da talakawa za su yi wa Kwankwaso halasci su taya shi kayar da ‘gwankin’ Arewa da ‘giwar’ kudu?

Babbar matsalar da siyasar Kwankwaso ke fuskanta, ita ce ta tawaye ko barambaram da tunanin sa ya yi da maganar nan da ake cewa, “ɗan Adam ba zai taɓa halaka ba, matuƙar ya san kan sa.”

Matsalar sa ita ce, ƙoƙarin da ya ke na ya zama abin da bai gama fahimta ba. A tunanin sa, a yau shi ne Malam Aminu Kanon wannan zamani. Sai dai bisa ga dukkan alamu, bai ma fahimci me Malam Aminu Kano ya rayu ya kuma mutu a kai ba. Kusan a iya cewa, ya yi wa abin ba wan ba ƙanin – karatun ɗankama. Domin kuwa, a haƙiƙanin gaskiya, da alama tun a babbaƙu ma aka jefara shi.

Ba zan ɓata lokaci a kan mene ne tunani da aƙida irin ta Malam Aminu ba, domin hakan zai iya ɗaukar mu wani dogon lokaci kafin mu gama. Amma zan mayar da himma ne a kan mummunar fahimtar da mutane ke yi wa tunani da aƙidar siyasa irin ta Malam.

Ɗaya daga cikin dalilan haɗa Kwankwaso da Malam Aminu shi ne, ɗaya daga cikin abubuwan da Kwankwaso ya fi bai wa muhimmanci shi ne, sanya jar hula kamar yadda Malam Aminu Kano shi ma a iya rayuwar sa yake sanya jar dara.

Sai dai ya manta, hakan ba ta taɓa zama wata alama ta mabiya Malam Aminu ba. A haƙiƙanin gaskiya ma, an fi kwaikwayon sanya sutura irin ta Rimi da ta Shagari a wannan zamani fiye da irin shigar Malam Aminu Kano.

Ba a nan kaɗai ta tsaya ba, wani tunani na Kwankwaso a kan Malam Aminu shi ne, ganin da ake siyasar Malam Aminu siyasa ce ta fitsara da tawaye ga magabata. Ko shakka babu, a wasu shekaru da su ka gabata, salon siyasar Malam Aminu Kano kenan, wanda har hakan ta sanya, Sarkin Kano Bayero ya taɓa ce masa “Malam Aminu ba ka ganin wata rana wannan abin da ku ka koya wa yara, zai fi ƙarfin ku?” Hakan kuwa ya faru, domin dawowa daga rakiyar irin waccan fahimta ta siyasa da Malam Aminu Kano ya yi, a zamanin da ya kafa jam’iyyar PRP, shi ne maƙasudin da ya janyo rikicin sa da Gwamnan Kano na wancan lokacin, marigayi Abubakar Rimi.

Sakamakon hakan ne ma ya janyo darewar jam’iyyar ta PRP, tsakanin Santsi da Taɓo. Wannan rikici ne ya janyo har Gwamna Rimi ya yi wata lacca da ya yi wa mutuncin Malam Aminu Kano hawan-ƙawarar da sai da Malam ɗin ya rubuta a wani kundin sa, “Ko shakka babu Rimi maƙiyi na ne.”

Idan muka yi la’akari da wannan, za mu iya hasashen irin haɗarin da Kwankwaso ke neman jefa kan sa, da kuma siyasar sa. Domin dai shi kan sa wanda ya ke ganin shi ya ke kwaikwayo, bai gama da aƙidar lafiya ba. Ta kai ga yaran da suka koya wa raini da cin zarafin magabata, da suka gama cin zarafin mutanen, sai suka koma kan su. To haka shi ma Kwankwaso, waɗannan yaran da yake nuna wa ba wanda ya isa sai shi, ranar da duk suka rasa wanda za su yi wa fitsara, kan sa za su dawo.

Wata babbar masifar da kuma sabon salon da Kwankwaso da Kwankwasiyya ke ƙoƙarin ɗora matasa a kai, ita ce siyasar daba da zubar da jini a Kano. Ko shakka babu, tarihi ya tabbatar da cewa, siyasar daba ta fara shigowa Kano ne, a zamanin NEPU, sakamakon halin da mabiyan ta suka tsinci kan su na rashin tsaro ga tarukkan su da su kan su ma. To amma hakan ba ta taɓa haifar wa Kano ɗa mai ido ba.

Daga irin kalaman da ke fitowa daga bakunan shi jagoran na Kwankwasiyya, da kuma wasu mabiyan sa, za ka tabbatar da cewa Kano na cikin wani garari, musamman a zaɓen gwamna.

A lokacin da ya shigo Kano, makonni biyu da suka gabata, Kwankwaso ya yi iƙirarin cewa, zai iya sanya mabiyan sa su shiga su ɗauko gwamna su cinye shi kamar karas. Wannan ba ƙaramin tunzura matasa ba ne. Domin ko ba komai, shi da yake maganar ya taɓa zama gwamna, ya kuma san illar da za ta biyo baya idan har hakan ta fara. Domin za a sanya Kano a cikin wani mummunan hali na rashin doka da oda, kuma shi kan sa ya san cewa, hukuma ba za ta yi masa da wasa ba, matukar hakan ta faru.

Wata babbar masifar da shi da kan sa ya ke iƙirari ita ce, batun da yake ta yayatawa na cewa, idan har Abba ya ci zaɓe, da kan sa zai hau katafila ya rushe dukkan wasu gine-gine da aka yi a filayen gwamnati. Sai dai ya manta da cewa, ko da Abba ya ci zaɓe, shi fa ba shi da wani muƙami da zai ba shi dama ya aikata haka.

Hukuma ce kawai ke da wannan ƙarfi, a kuma hukumance babu muƙamin ka-fi-gwamna. Yin hakan zai iya janyo rikicin da zai iya jefa Kano da tattalin arzikin ta cikin wani mummunan hali.

Irin waɗannan kalamai da ke fitowa daga bakin sa, su suka bai wa mabiyan sa ƙwarin guiwar, ɗaukar aniyar idan dai ba su suka ci zaɓe ba, to kuwa sai dai a fasa kowa ya rasa. Ɗaya daga cikin zaɓaɓɓun ‘yan majalisar tarayya da aka zaɓa daga Karamar Hukumar Kiru da Bebeji, wato Abdulmuminu Jibrin Kofa, ya sa yake cewa, “Duk wani jami’in zaɓe da muka kama yana neman ya yi mana maguɗi, to za a ga shigar sa Bebeji, amma ba za a ga fitar sa ba.” Hakan na nuni da shirin mabiya Kwankwasiyyar na su ɗauki doka a hannun su. Idan kuwa har hukuma ta zura ido, hakan ta faru, kuma hukuma ta zura ido, to kuwa an ɗra ƙasar nan a kan wani tsari mafi muni, wanda zai iya jefa ƙasar nan cikin mummunan hali.

Allah ya kyauta mana!

Mamman marubuci ne, ya rubuto daga Kano.

Tags: AminuHausaKanoKwankwasoLabaraiNewsNNPPRabiu
Previous Post

BAUCHI TA ƊAU ZAFI: Yadda rikicin siyasa tsakanin magoya bayan PDP da APC ya yi sanadiyyar ran Shata a Bauchi

Next Post

KANO 2023: Ko Kwankwasiyya za ta saɓule wandon butulcin Gandujiyya, ta gama da guma-guman ‘aikin Gama’?

Premium Times Hausa

Premium Times Hausa

Next Post
KANO 2023: Ko Kwankwasiyya za ta saɓule wandon butulcin Gandujiyya, ta gama da guma-guman ‘aikin Gama’?

KANO 2023: Ko Kwankwasiyya za ta saɓule wandon butulcin Gandujiyya, ta gama da guma-guman 'aikin Gama'?

Discussion about this post

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • Ba ni kaɗai ne na fidda sunan Ahmed Lawan ya yi takarar shugaban kasa da Tinubu ba, akwai wasu da ke bayan fage – Adamu
  • Yadda bashin da Chana ta hana Najeriya ya kawo cikas a noman shinkafa, da aikin titin jirgin ƙasan Ibadan zuwa Kano
  • SHEKARU 63 BAYAN SAMUN ‘YANCI: ‘Ban so Najeriya ta afka cikin raɗaɗin ƙuncin da ake fama da shi ba’ – Tinubu
  • SHEKARU 63 BAYAN SAMUN ‘YANCI: ‘Za yi wa masu ƙaramin albashi ƙarin Naira 25,000 tsawon watanni 6 a jere
  • SHEKARU 63 BAYAN SAMUN ‘YANCI: Fassarar Jawabin Shugaba Tinubu:

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.