Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa Atiku Abubakar, wanda ya zo na biyu a zaɓen shugaban ƙasa, ya kafa gaggan lauyoyin da ya bai wa aikin ƙwato masa nasarar da ya yi iƙirarin cewa shi ne ya ci zaɓen ranar 25 Ga Fabrairu.
Ya ce ya na so su ƙwato masa haƙƙin sa, kuma hakan a cewar sa zai zamo wani ginshiƙin ƙarfafa dimokraɗiyya a Najeriya.
Yayin da ya ke wa lauyoyin jawabi a hedikwatar kamfen ɗin sa, lauyoyin waɗanda ke ƙarƙashin jagorancin Babban Lauya Joe Gadzama, Atiku ya shaida masu cewa su iyakar ƙoƙarin su wajen ƙwato masa haƙƙi, ba don shi kaɗai ba, kuma ba don PDP ba, sai don hakan zai ƙara wa dimokraɗiyya daraja, kuma zai ƙara tsaftace tsarin zaɓe, kuma hakan zai zama alheri har ga yaran da za a haifa shekaru masu zuwa.
Sauran lauyoyin da Atiku ya ɗauka sun haɗa da Chris Uche, Paul Usoro, Tayo Jegede, Mike Ozekhome, Mahmood Magaji, Joe Abraham, Chukwuma Umeh, Garba Tetengi da kuma Emeka Etiaba, waɗanda dukkan su Manyan Lauyoyi ne, wato SAN.
Sauran sun haɗa da Goddy Uche, Maxwell Gidado, A.K Ajibade, O. M Atayebi, Nella Rabana, Paul Ogbole, Nuremi Jimoh da kuma Abdul Ibrahim, su ma duk manyan lauyoyi ne, SAN.
Idan ba a manta ba, Kotun Ɗaukaka Ƙara ta bai wa Atiku Abubakar da Peter Obi na LP iznin binciken ƙwaƙwaf kan na’urorin BVAS da aka yi zaɓen shugaban ƙasa a kan zargin an yi amfani da BVAS ɗin aka yi masu maguɗi.
INEC Ta Garzaya Kotu A Kan Na’urar BVAS:
A na ta ɓangaren, INEC INEC ta nemi kotu iznin yi wa na’urorin BVAS garambawul kafin zaɓen gwamnoni.
Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), ta garzaya Kotun Ɗauka Ƙara domin neman iznin yi wa na’urorin tantance masu rajistar zaɓe (BVAS) garambawul, kafin zaɓen ranar 11 ga Maris.
Za a yi zaɓen gwamnoni da na majalisar dokoki jihohi a ranar Asabar, 11 ga Maris.
INEC ta garzaya kotun ne kwana biyu bayan kotu ta bai wa Atiku Abubakar na PDP da Peter Obi na LP iznin binciken na’urorin BVAS waɗanda aka yi zaɓen shugaban ƙasa da na majalisar tarayya da su.
Sun nemi iznin ne domin su ƙara kafa wa kotun hujjojin da su ke dogaro da su dangane da zargin maguɗin da su ke cewa an yi a zaɓen ranar 25 ga Fabrairu.
Sai dai kuma INEC ta je Kotun Ɗaukaka Ƙara ta na neman a ɗage mata hukuncin hana ta taɓa na’urorin BVAS bayan zaɓen shugaban ƙasa.
Kotun ta hana INEC taɓa su ne, saboda ta bai wa PDP da LP iznin binciken na’urorin domin su gano zargin maguɗin da su ke iƙirarin an yi, idan har an yi ɗin.
Sai dai kuma kwanaki biyu bayan an bai wa su Atiku iznin binciken BVAS, ita ma INEC ta garzaya Kotun Ɗaukaka Ƙara ta nemi iznin cewa a ba ta damar yi wa na’urorin garambawul saboda da su ne za ta yi aikin tantance masu zaɓen ranar 11 ga Maris.
INEC ta ce idan ba ta yi masu garambawul ɗin ba da wuri saboda an ce ta nesance su, tunda an bai wa Atiku da Obi iznin binciken su, to sai dai fa idan ɗage zaɓen gwamnoni da na majalisar dokoki za ta yi.
Ta kafa hujjar cewa ba a Abuja ake aikin yi wa na’urorin garambawul ba, kuma aikin ya na ɗaukar lokaci.
PREMIUM TIMES ta buga labarin yadda kotu ta bai wa Atiku da Obi iznin duba na’urorin aikin zaɓen INEC.
Kotun Ɗaukaka Ƙara ta Abuja ta bai wa ɗan takarar shugaban ƙasa Atiku Abubakar da takwaran sa Peter Obi iznin binciken na’urorin da Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta yi amfani da su wajen gudanar da zaɓen shugaban ƙasa a 2023.
Atiku na PDP da Obi na LP sun ƙi amincewa da sakamakon zaɓen shugaban ƙasa na da Majalisar Dattawa da ta Tarayya.
Su biyun dai Bola Tinubu ne na APC INEC ta bayyana cewa ya yi nasara a kan su.
Su biyun dai kowa ya shigar da ta sa ƙarar daban-daban, wadda su ka ce INEC ba ta bi doka wajen tattara sakamakon zaɓe ba.
Ɓangarorin biyu sun nemi kotu ta ba su iznin binciken na’urorin da INEC ta yi amfani da su wajen zaɓe.
Sun ce binciken na’urorin zai taimaka masu wajen yi wa kotu bayanin irin ƙarar da za su shigar da kuma ƙara bijiro da hujjojin da za su gabatar wa kotu.
Idan za a iya tunawa, tun kafin a kai ga bayyana sakamakon zaɓe shi ma tsohon Shugaban Ƙasa, Olusegun Obasanjo ya ce akwai harƙalla a zaɓen shugaban ƙasa, amma a kai zuciya nesa.
Tsohon Shugaban Ƙasa Olusegun Obasanjo ya yi zargin cewa an cukurkuɗa sakamakon zaɓen shugaban ƙasa.
Obasanjo ya yi kira ga Shugaba Muhammadu Buhari ya sa sake bibiyar gaba ɗayan yadda aka tattara sakamakon zaɓen.
Haka Obasanjo ya bayyana a cikin wata wasiƙar da shi da kan sa ya sa wa hannu a ranar Litinin.
Ya yi zargin cewa “yawancin sakamakon zaben da aka tattara ba tare da na’urar tantance masu katin shaidar rajistar zaɓe (BVAS da Manhajar Tattara Sakamakon Zaɓe (Server) ba, ba su nuna haƙiƙanin gaskiyar abin da ‘yan Najeriya su ka zaɓa ba.”
Obasanjo dai na ɗaya daga cikin masu goyon bayan jam’iyyar LP, wadda Peter Obi ne ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar.
PREMIUM TIMES ta ruwaito cewa jam’iyyar LP da PDP da wasu ‘yan adawa sun fice daga Cibiyar Tattara Sakamakon Zaɓe ta INEC a Abuja, a ranar Litinin.
Sun fice ne bayan sun zargi INEC da ƙin sakin sakamakon zaɓe a manhajar iREV.
Jam’iyyun sun ce ƙin fitar da sakamakon a iREV kamar yadda Dokar INEC ta tilasta a yi, ya nuna cewa akwai alamun zai yiwu a damalmala lissafin ƙuri’un.
A cikin sanarwar Obasanjo, ya jinjina wa Buhari a kan matsayin da ya ɗauka na tabbatar da cewa ya bar wa Najeriya gadon sahihin zaɓe.
Sai dai kuma ya yi kira ga Buhari ya ceto ƙasar nan daga hatsarin da ta ka iya faɗawa sakamakon zaɓe.
Haka a wani labarin, PREMIUM TIMES ta buga labarin yadda PDP ta ƙi amincewa da sakamakon yawan ƙuri’un Peter Obi a Legas.
Jam’iyyar PDP ta bayyana cewa ba ta amince da sakamakon yawan ƙuri’un da jam’iyyar LP ta Peter Obi ta samu a Jihar Legas ba.
Tsohon Shugaban Jam’iyyar PDP na Legas, Tunji Shelle wanda kuma shi ne ejan ɗin PDP wurin tattara sakamakon zabe a Yaba, Legas, ya ce “an yi ƙumbiya-ƙumbiya gabaɗayan aikin tattara ƙuri’un.”
“Ban amince da sakamakon zaɓen ba, kuma na ɗauki wannan matsaya ce a madadin jam’iyyar da na ke wakilta, PDP.” Haka Shelle ya bayyana wajen tattara sakamakon zaɓen a ranar Litinin.
“Ban amince da sakamakon da LP ta samu ba, ba wai don ba mu yi nasara ba. Amma saboda an saye waɗanda aka saye aka yi mana ƙumbiya-ƙumbiya.”
Peter Obi na LP dai ya lashe yawan ƙuri’un jihar Legas har 582,454, shi kuma Bola Tinubu na APC 572,606.
Atiku Abubakar na PDP ya samu 75,750.
“Ba na jin INEC ta bayar da kyakkyawan horon aikin zaɓe ga ma’aikatan wucin-gadin da ta ɗauka. Saboda a gaskiya ba mu shirya wa fara aiki da na’urar tantance masu rajistar zaɓe ba, wato BVAS. Saboda a wurin tantancewar ne ake yin amaja. Da yawan sakamakon zaɓen duk ba a ma loda su a BVAS ɗin. Amma haka aka fitar da sakamako.”
Ya ce kamata ya yi BVAS ya tsaftace aikin zaɓe, amma maimakon haka, sai ma ya ƙara maida hannun agogo baya.