• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Janar Diya, tsohon Mataimakin Janar Abacha ya rasu

    Janar Diya, tsohon Mataimakin Janar Abacha ya rasu

    Kashim Shettima of Borno

    SHARI’AR ZARGIN SHETTIMA YA FITO TAKARA WURI BIYU: Kotu ta kori ƙarar da PDP ta nemi a soke takarar Tinubu da Shettima

    ZAƁEN KANO: Ganduje, Gawuna Garo da APC sun ƙi amincewa da sakamakon zaɓe, sun yi zanga-zanga a Kano

    ZAƁEN KANO: Ganduje, Gawuna Garo da APC sun ƙi amincewa da sakamakon zaɓe, sun yi zanga-zanga a Kano

    Ba ayi zabe a Katsina ba, coge aka yi kuma za mu garzaya Kotu – Lado-Danmarke

    Ba ayi zabe a Katsina ba, coge aka yi kuma za mu garzaya Kotu – Lado-Danmarke

    Hyacinth Alia na APC ya lashe zaben gwamnan jihar Benuwai

    Hyacinth Alia na APC ya lashe zaben gwamnan jihar Benuwai

    Umar Bago na APC ya lashe zaben gwamnan Neja

    Umar Bago na APC ya lashe zaben gwamnan Neja

    KURUNKUS: Abba Gida-Gida ya doke ɗan takaran Uban Abba, Gawuna na APC da kuri’u sama da miliyan ɗaya a Zaɓen gwamnan Kano

    KURUNKUS: Abba Gida-Gida ya doke ɗan takaran Uban Abba, Gawuna na APC da kuri’u sama da miliyan ɗaya a Zaɓen gwamnan Kano

    ZAƁEN GWAMNAN JIGAWA: Namadin APC ya natsar da Lamidon PDP a Jigawa, ya lallasa shi da kuri’u 618,449

    ZAƁEN GWAMNAN JIGAWA: Namadin APC ya natsar da Lamidon PDP a Jigawa, ya lallasa shi da kuri’u 618,449

    Thugs-attack-collation

    ZAƁEN GWAMNONI YA ƊAU ZAFI: An kashe shugaban PDP bayan an lakaɗa masa dukan tsiya a rumfar zaɓen sa

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Janar Diya, tsohon Mataimakin Janar Abacha ya rasu

    Janar Diya, tsohon Mataimakin Janar Abacha ya rasu

    Kashim Shettima of Borno

    SHARI’AR ZARGIN SHETTIMA YA FITO TAKARA WURI BIYU: Kotu ta kori ƙarar da PDP ta nemi a soke takarar Tinubu da Shettima

    ZAƁEN KANO: Ganduje, Gawuna Garo da APC sun ƙi amincewa da sakamakon zaɓe, sun yi zanga-zanga a Kano

    ZAƁEN KANO: Ganduje, Gawuna Garo da APC sun ƙi amincewa da sakamakon zaɓe, sun yi zanga-zanga a Kano

    Ba ayi zabe a Katsina ba, coge aka yi kuma za mu garzaya Kotu – Lado-Danmarke

    Ba ayi zabe a Katsina ba, coge aka yi kuma za mu garzaya Kotu – Lado-Danmarke

    Hyacinth Alia na APC ya lashe zaben gwamnan jihar Benuwai

    Hyacinth Alia na APC ya lashe zaben gwamnan jihar Benuwai

    Umar Bago na APC ya lashe zaben gwamnan Neja

    Umar Bago na APC ya lashe zaben gwamnan Neja

    KURUNKUS: Abba Gida-Gida ya doke ɗan takaran Uban Abba, Gawuna na APC da kuri’u sama da miliyan ɗaya a Zaɓen gwamnan Kano

    KURUNKUS: Abba Gida-Gida ya doke ɗan takaran Uban Abba, Gawuna na APC da kuri’u sama da miliyan ɗaya a Zaɓen gwamnan Kano

    ZAƁEN GWAMNAN JIGAWA: Namadin APC ya natsar da Lamidon PDP a Jigawa, ya lallasa shi da kuri’u 618,449

    ZAƁEN GWAMNAN JIGAWA: Namadin APC ya natsar da Lamidon PDP a Jigawa, ya lallasa shi da kuri’u 618,449

    Thugs-attack-collation

    ZAƁEN GWAMNONI YA ƊAU ZAFI: An kashe shugaban PDP bayan an lakaɗa masa dukan tsiya a rumfar zaɓen sa

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

Atiku ya kafa gaggan lauyoyi 18, ya ce su tashi tsaye su ƙwato masa ‘nasarar zaɓen sa’ daga hannun Tinubu

Mohammed LerebyMohammed Lere
March 8, 2023
in Manyan Labarai
0
Atiku ya kafa gaggan lauyoyi 18, ya ce su tashi tsaye su ƙwato masa ‘nasarar zaɓen sa’ daga hannun Tinubu

Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa Atiku Abubakar, wanda ya zo na biyu a zaɓen shugaban ƙasa, ya kafa gaggan lauyoyin da ya bai wa aikin ƙwato masa nasarar da ya yi iƙirarin cewa shi ne ya ci zaɓen ranar 25 Ga Fabrairu.

Ya ce ya na so su ƙwato masa haƙƙin sa, kuma hakan a cewar sa zai zamo wani ginshiƙin ƙarfafa dimokraɗiyya a Najeriya.

Yayin da ya ke wa lauyoyin jawabi a hedikwatar kamfen ɗin sa, lauyoyin waɗanda ke ƙarƙashin jagorancin Babban Lauya Joe Gadzama, Atiku ya shaida masu cewa su iyakar ƙoƙarin su wajen ƙwato masa haƙƙi, ba don shi kaɗai ba, kuma ba don PDP ba, sai don hakan zai ƙara wa dimokraɗiyya daraja, kuma zai ƙara tsaftace tsarin zaɓe, kuma hakan zai zama alheri har ga yaran da za a haifa shekaru masu zuwa.

Sauran lauyoyin da Atiku ya ɗauka sun haɗa da Chris Uche, Paul Usoro, Tayo Jegede, Mike Ozekhome, Mahmood Magaji, Joe Abraham, Chukwuma Umeh, Garba Tetengi da kuma Emeka Etiaba, waɗanda dukkan su Manyan Lauyoyi ne, wato SAN.

Sauran sun haɗa da Goddy Uche, Maxwell Gidado, A.K Ajibade, O. M Atayebi, Nella Rabana, Paul Ogbole, Nuremi Jimoh da kuma Abdul Ibrahim, su ma duk manyan lauyoyi ne, SAN.

Idan ba a manta ba, Kotun Ɗaukaka Ƙara ta bai wa Atiku Abubakar da Peter Obi na LP iznin binciken ƙwaƙwaf kan na’urorin BVAS da aka yi zaɓen shugaban ƙasa a kan zargin an yi amfani da BVAS ɗin aka yi masu maguɗi.

INEC Ta Garzaya Kotu A Kan Na’urar BVAS:

A na ta ɓangaren, INEC INEC ta nemi kotu iznin yi wa na’urorin BVAS garambawul kafin zaɓen gwamnoni.

Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), ta garzaya Kotun Ɗauka Ƙara domin neman iznin yi wa na’urorin tantance masu rajistar zaɓe (BVAS) garambawul, kafin zaɓen ranar 11 ga Maris.

Za a yi zaɓen gwamnoni da na majalisar dokoki jihohi a ranar Asabar, 11 ga Maris.

INEC ta garzaya kotun ne kwana biyu bayan kotu ta bai wa Atiku Abubakar na PDP da Peter Obi na LP iznin binciken na’urorin BVAS waɗanda aka yi zaɓen shugaban ƙasa da na majalisar tarayya da su.

Sun nemi iznin ne domin su ƙara kafa wa kotun hujjojin da su ke dogaro da su dangane da zargin maguɗin da su ke cewa an yi a zaɓen ranar 25 ga Fabrairu.

Sai dai kuma INEC ta je Kotun Ɗaukaka Ƙara ta na neman a ɗage mata hukuncin hana ta taɓa na’urorin BVAS bayan zaɓen shugaban ƙasa.

Kotun ta hana INEC taɓa su ne, saboda ta bai wa PDP da LP iznin binciken na’urorin domin su gano zargin maguɗin da su ke iƙirarin an yi, idan har an yi ɗin.

Sai dai kuma kwanaki biyu bayan an bai wa su Atiku iznin binciken BVAS, ita ma INEC ta garzaya Kotun Ɗaukaka Ƙara ta nemi iznin cewa a ba ta damar yi wa na’urorin garambawul saboda da su ne za ta yi aikin tantance masu zaɓen ranar 11 ga Maris.

INEC ta ce idan ba ta yi masu garambawul ɗin ba da wuri saboda an ce ta nesance su, tunda an bai wa Atiku da Obi iznin binciken su, to sai dai fa idan ɗage zaɓen gwamnoni da na majalisar dokoki za ta yi.

Ta kafa hujjar cewa ba a Abuja ake aikin yi wa na’urorin garambawul ba, kuma aikin ya na ɗaukar lokaci.

PREMIUM TIMES ta buga labarin yadda kotu ta bai wa Atiku da Obi iznin duba na’urorin aikin zaɓen INEC.

Kotun Ɗaukaka Ƙara ta Abuja ta bai wa ɗan takarar shugaban ƙasa Atiku Abubakar da takwaran sa Peter Obi iznin binciken na’urorin da Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta yi amfani da su wajen gudanar da zaɓen shugaban ƙasa a 2023.

Atiku na PDP da Obi na LP sun ƙi amincewa da sakamakon zaɓen shugaban ƙasa na da Majalisar Dattawa da ta Tarayya.

Su biyun dai Bola Tinubu ne na APC INEC ta bayyana cewa ya yi nasara a kan su.

Su biyun dai kowa ya shigar da ta sa ƙarar daban-daban, wadda su ka ce INEC ba ta bi doka wajen tattara sakamakon zaɓe ba.

Ɓangarorin biyu sun nemi kotu ta ba su iznin binciken na’urorin da INEC ta yi amfani da su wajen zaɓe.

Sun ce binciken na’urorin zai taimaka masu wajen yi wa kotu bayanin irin ƙarar da za su shigar da kuma ƙara bijiro da hujjojin da za su gabatar wa kotu.

Idan za a iya tunawa, tun kafin a kai ga bayyana sakamakon zaɓe shi ma tsohon Shugaban Ƙasa, Olusegun Obasanjo ya ce akwai harƙalla a zaɓen shugaban ƙasa, amma a kai zuciya nesa.

Tsohon Shugaban Ƙasa Olusegun Obasanjo ya yi zargin cewa an cukurkuɗa sakamakon zaɓen shugaban ƙasa.

Obasanjo ya yi kira ga Shugaba Muhammadu Buhari ya sa sake bibiyar gaba ɗayan yadda aka tattara sakamakon zaɓen.

Haka Obasanjo ya bayyana a cikin wata wasiƙar da shi da kan sa ya sa wa hannu a ranar Litinin.

Ya yi zargin cewa “yawancin sakamakon zaben da aka tattara ba tare da na’urar tantance masu katin shaidar rajistar zaɓe (BVAS da Manhajar Tattara Sakamakon Zaɓe (Server) ba, ba su nuna haƙiƙanin gaskiyar abin da ‘yan Najeriya su ka zaɓa ba.”

Obasanjo dai na ɗaya daga cikin masu goyon bayan jam’iyyar LP, wadda Peter Obi ne ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar.

PREMIUM TIMES ta ruwaito cewa jam’iyyar LP da PDP da wasu ‘yan adawa sun fice daga Cibiyar Tattara Sakamakon Zaɓe ta INEC a Abuja, a ranar Litinin.

Sun fice ne bayan sun zargi INEC da ƙin sakin sakamakon zaɓe a manhajar iREV.

Jam’iyyun sun ce ƙin fitar da sakamakon a iREV kamar yadda Dokar INEC ta tilasta a yi, ya nuna cewa akwai alamun zai yiwu a damalmala lissafin ƙuri’un.

A cikin sanarwar Obasanjo, ya jinjina wa Buhari a kan matsayin da ya ɗauka na tabbatar da cewa ya bar wa Najeriya gadon sahihin zaɓe.

Sai dai kuma ya yi kira ga Buhari ya ceto ƙasar nan daga hatsarin da ta ka iya faɗawa sakamakon zaɓe.

Haka a wani labarin, PREMIUM TIMES ta buga labarin yadda PDP ta ƙi amincewa da sakamakon yawan ƙuri’un Peter Obi a Legas.

Jam’iyyar PDP ta bayyana cewa ba ta amince da sakamakon yawan ƙuri’un da jam’iyyar LP ta Peter Obi ta samu a Jihar Legas ba.

Tsohon Shugaban Jam’iyyar PDP na Legas, Tunji Shelle wanda kuma shi ne ejan ɗin PDP wurin tattara sakamakon zabe a Yaba, Legas, ya ce “an yi ƙumbiya-ƙumbiya gabaɗayan aikin tattara ƙuri’un.”

“Ban amince da sakamakon zaɓen ba, kuma na ɗauki wannan matsaya ce a madadin jam’iyyar da na ke wakilta, PDP.” Haka Shelle ya bayyana wajen tattara sakamakon zaɓen a ranar Litinin.

“Ban amince da sakamakon da LP ta samu ba, ba wai don ba mu yi nasara ba. Amma saboda an saye waɗanda aka saye aka yi mana ƙumbiya-ƙumbiya.”

Peter Obi na LP dai ya lashe yawan ƙuri’un jihar Legas har 582,454, shi kuma Bola Tinubu na APC 572,606.

Atiku Abubakar na PDP ya samu 75,750.

“Ba na jin INEC ta bayar da kyakkyawan horon aikin zaɓe ga ma’aikatan wucin-gadin da ta ɗauka. Saboda a gaskiya ba mu shirya wa fara aiki da na’urar tantance masu rajistar zaɓe ba, wato BVAS. Saboda a wurin tantancewar ne ake yin amaja. Da yawan sakamakon zaɓen duk ba a ma loda su a BVAS ɗin. Amma haka aka fitar da sakamako.”

Ya ce kamata ya yi BVAS ya tsaftace aikin zaɓe, amma maimakon haka, sai ma ya ƙara maida hannun agogo baya.

Tags: AbujaAtikuHausaLauyoyiNewsPREMIUM TIMES
Previous Post

BAKI SHI KE YANKA WUYA: An gurfanar da matar da ta zargi gwamna sukutum da kwartanci, har da zargin lalata da kwamishinar sa

Next Post

KASUWAR MANYAN LAUYOYI TA BUƊE: APC ta naɗa kintima-kintiman lauyoyin taya Tinubu gumurzu da Atiku da Obi a kotu

Next Post
Lawyers

KASUWAR MANYAN LAUYOYI TA BUƊE: APC ta naɗa kintima-kintiman lauyoyin taya Tinubu gumurzu da Atiku da Obi a kotu

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • RIKICIN PDP: ‘Ina alfahari da ‘anti-fatin’ da na yi wa PDP, daga yau mun koya wa su O’o hankali -Anyin Pius Anyim
  • Janar Diya, tsohon Mataimakin Janar Abacha ya rasu
  • ‘Yan sanda sun ce gidan da mafusata su ka kai wa hari a Bauchi ba na Shugaban INEC ba ne
  • SHARI’AR ZARGIN SHETTIMA YA FITO TAKARA WURI BIYU: Kotu ta kori ƙarar da PDP ta nemi a soke takarar Tinubu da Shettima
  • SABON RIKICIN PDP: ‘Ko dai ka janye dakatarwar da ka yi min, ko na fice na bar maka jam’iyyar’ -Gargaɗin Shema ga Ayu

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.