Gwamanti Tarayya ta bayyana cewa har yau ba ta kammala tsare-tsaren bijiro da hanyoyin da za ta rage wa talakawa tsadar rayuwa ba, domin rage masu raɗaɗin tsadar fetur a duk lokacin da aka cire tallafin fetur.
Ƙaramin Ministan Kasafin Kuɗaɗe da Tsare-tsare na Ƙasa, Clement Agba ne ya bayyana haka, yayin da ya ke wa manema labarai bayani a ranar Laraba.
Ya yi masu bayanin ne a Fadar Shugaban Ƙasa, bayan tashi daga taron Majalisar Zartaswa a Abuja.
Gwamnatin Tarayya dai ta amince a kashe Naira tiriliyan 3.3 wajen biyan kuɗaɗen tallafin fetur tsakanin Janairu zuwa Yuni, 2023.
Agba ya ce an kafa kwamiti wanda Mataimakin Shugaban Ƙasa ke jagoranta, wato Yemi Osinbajo, kuma ya na aiki kafaɗa da kafaɗa da Majalisar Tattalin Arziki ta Ƙasa (NEC).
Kwamitin ya ƙunshi gwamnonin jihohi 36 da kuma Ministan Abuja, su na kan aikin yadda za a bijiro da hanyoyin sauƙaƙa wa ‘yan Najeriya tsadar rayuwar da za a tunkara nan gaba kaɗan idan an cire tallafin fetur.
Cikin watan Fabrairu ne dai Shugaban NNPCL ya ce Najeriya na kashe Naira biliyan 400 duk wata wajen cike giɓin tallafin fetur.
Shugaban NNPCL Mele Kyari ya ce a duk wata Najeriya ta na kashe fiye da naira biliyan 400 wajen biyan kuɗin tallafin fetur.
Kyari ya ce tuni NNPCL ce kaɗai ke sayo fetur daga waje tsawon shekaru, kuma NNPCL ɗin ne ke jin jikin biyan ɗoriyar maƙudan kuɗaɗe da sunan cike giɓin tallafin fetur.
Ya ce sauran kamfanoni sun daina shigo da fetur saboda wahalar da suke fuskanta kafin samun canjin dalilin Amurka da za su buƙata kafin su sayo fetur ɗin a waje.
“Har a kwanaki uku da su ka gabata, idan NNPLC ya sayo fetur a waje, to duk lita ɗaya ta na tashi a kan N315 daga cinikin sa, lodin sa, ɗauko shi zuwa sauke shi. Mu kuma mu sakar wa kwastomomin mu kan naira 113. Kenan akwai bambancin naira 202 a kowace lita kenan mu ka shigo da ita cikin ƙasar nan.
“Idan aka lissafa asarar kuɗin tallafin lita ɗaya naira 202 sau lita miliyan 66.5, sannan a yi sau 30 na kwanan wata, to za a ga a duk wata ana asarar biyan naira biliyan 400 kenan.”
Kyari ya ce duk da kuɗin tallafi na cikin kasafin kuɗi, amma haka NNPCL ke ci gaba da biyan kuɗaɗen ba tare da Ma’aikatar Harkokin Kuɗaɗe da Kasafi na biyan ta abin da ya ke kashewa ba.
Kyari ya ce NNPCL na fuskantar matsanancin ƙalubalen rashin tara kuɗaɗen shiga, saboda waɗanda ta ke tarawa ɗin su na tafiya wajen cike giɓin tallafin fetur, alhali kuma Ma’aikatar Harkokin Kuɗaɗe ba ta biyan NNPCL abin da ya ke kashewa duk wata.