A Jihar Katsina Rundunar ‘Yan Sanda ta damƙe wasu matasa 15 da aka samu tare da sabbin kwamfutoci.
Kakakin Yaɗa Labaran ‘Yan Sandan Jihar Katsina, Gambo Isah, ya tabbatar wa PREMIUM TIMES kama matasan.
Sai dai ya ce ba gaskiya ba ne da ake yaɗa cewa an kama su da tulin ƙuri’u.
Ya ce an kama su da kwamfutoci laptop, waɗanda ake masu zargin cewa za su kutsa ne domin leƙen sakamakon zaɓe ko kuma baddala sakamakon.
Wata majiya ta bayyana wa wakilin mu cewa dukkan kwamfutocin da jami’an tsaron su ka kama a hannun matasan akwai tambarin wata jam’iyyar siyasa jikin ta.